ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Ɗauki Matakin Ƙwace Wasu Gidajen Abubakar Malami A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 months ago
EFCC

Jami’an (EFCC) a jiya sun rufe gidajen tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami (SAN), da ke Abuja.

Hakan na zuwa ne yayin da (ICPC) ta sanar da shirin gurfanar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban kotu a yau kan zargin almundahanar kudade.

  • Saraki Ya Soki Gwamnatin Kwara Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro
  • Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

An ga wasu jami’an EFCC sanye da kayan farar hula suna sanya alama a gidajen Malami da ke Maitama, Abuja, a ranar Litinin, lamarin da ya jawo zanga-zanga daga bangaren tsohon AGF din, inda ya tambayi sahihancin takardun da jami’an suka gabatar.

ADVERTISEMENT

A yayin cacar baki da ta biyo baya, jami’an EFCC sun dage cewa takardun da suka kawo na umarnin kotu ne ingantattu, duk da korafin da Malami ya rika yi akai-akai.

“Ku nuna min inda aka ce ku zo ku kwace dukiyata… alhali shari’ar na gaban kotu, shin za ku iya yin hakan ba bisa ka’ida ba? Shin yana karkashin kwace dukiya ne bayan umarnin ya kare? Umarnin da aka bayar na kwanaki 14 ya riga ya kare, amma kuna zuwa ku kunyata ni.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Tun da sassafe kuna wani gidana, yanzu kuma kuna nan.

Ina umarnin da ya ba ku izinin zuwa kan dukiyata ku yi musu alama? Wannan umarnin nake son gani. Ku nuna min inda aka ce za ku iya zuwa ku yi alama a kan dukiyata. Prince (ya juya ga wani jami’in EFCC), ina umarnin? Umarnin nan ba ya bayyana a fili cewa kuna da izinin zuwa ku yi alama a kan dukiyata. Wannan lamari yana gaban kotu.

Ina umarnin kotu da ya ba ku izini? Shin kun zo ne don ku kunyata ni ba tare da dalili ba…? Ba tare da wani ingantaccen umarnin kotu ba, alhali shari’ar na gaban kotu, kuna zuwa kan dukiyata don ku kunyata ni. Haka ake yi ne? To, ku ci gaba ku yi alamar. Za mu hadu a kotu,” in ji Malami.

Sai dai an ji jami’in EFCC yana cewa, “Muna da ikon yin alama a kan dukiya idan tana karkashin dukiyar da za a kwace. Ga umarnin; na ba ka umarnin, ranka ya dade.”

A wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TB a ranar Litinin, Malami ya kara bayani kan rufe gidajensa, inda ya ce ya kalubalanci umarnin kotu da ke neman a yi kwacewar wucin gadi na dukiyoyinsa.

Ya ce, “Akwai jami’ai da suka zo sanye da kayan aiki cikakke, dauke da makamai, kuma sun kasance masu tsoratarwa da cin zarafi ga ‘yan uwana na kusa, har ma suna cewa sun zo ne don kai wasikun gayyata.

Daga karshe dai an bayar da wasikun, ba kawai a gidan da suka same ni ba, har ma da sauran gidaje na da wuraren kasuwanci na, duk an kai hari a yau (Litinin), 23 ga Maris, 2026, daga jami’an da suka ce sun fito daga EFCC.”

EFCC
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
EFCC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Yi Murabus

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Yi Murabus

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.