ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Ɗauki Matakin Ƙwace Wasu Gidajen Abubakar Malami A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
EFCC

Jami’an (EFCC) a jiya sun rufe gidajen tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami (SAN), da ke Abuja.

Hakan na zuwa ne yayin da (ICPC) ta sanar da shirin gurfanar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban kotu a yau kan zargin almundahanar kudade.

  • Saraki Ya Soki Gwamnatin Kwara Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro
  • Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

An ga wasu jami’an EFCC sanye da kayan farar hula suna sanya alama a gidajen Malami da ke Maitama, Abuja, a ranar Litinin, lamarin da ya jawo zanga-zanga daga bangaren tsohon AGF din, inda ya tambayi sahihancin takardun da jami’an suka gabatar.

ADVERTISEMENT

A yayin cacar baki da ta biyo baya, jami’an EFCC sun dage cewa takardun da suka kawo na umarnin kotu ne ingantattu, duk da korafin da Malami ya rika yi akai-akai.

“Ku nuna min inda aka ce ku zo ku kwace dukiyata… alhali shari’ar na gaban kotu, shin za ku iya yin hakan ba bisa ka’ida ba? Shin yana karkashin kwace dukiya ne bayan umarnin ya kare? Umarnin da aka bayar na kwanaki 14 ya riga ya kare, amma kuna zuwa ku kunyata ni.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Tun da sassafe kuna wani gidana, yanzu kuma kuna nan.

Ina umarnin da ya ba ku izinin zuwa kan dukiyata ku yi musu alama? Wannan umarnin nake son gani. Ku nuna min inda aka ce za ku iya zuwa ku yi alama a kan dukiyata. Prince (ya juya ga wani jami’in EFCC), ina umarnin? Umarnin nan ba ya bayyana a fili cewa kuna da izinin zuwa ku yi alama a kan dukiyata. Wannan lamari yana gaban kotu.

Ina umarnin kotu da ya ba ku izini? Shin kun zo ne don ku kunyata ni ba tare da dalili ba…? Ba tare da wani ingantaccen umarnin kotu ba, alhali shari’ar na gaban kotu, kuna zuwa kan dukiyata don ku kunyata ni. Haka ake yi ne? To, ku ci gaba ku yi alamar. Za mu hadu a kotu,” in ji Malami.

Sai dai an ji jami’in EFCC yana cewa, “Muna da ikon yin alama a kan dukiya idan tana karkashin dukiyar da za a kwace. Ga umarnin; na ba ka umarnin, ranka ya dade.”

A wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TB a ranar Litinin, Malami ya kara bayani kan rufe gidajensa, inda ya ce ya kalubalanci umarnin kotu da ke neman a yi kwacewar wucin gadi na dukiyoyinsa.

Ya ce, “Akwai jami’ai da suka zo sanye da kayan aiki cikakke, dauke da makamai, kuma sun kasance masu tsoratarwa da cin zarafi ga ‘yan uwana na kusa, har ma suna cewa sun zo ne don kai wasikun gayyata.

Daga karshe dai an bayar da wasikun, ba kawai a gidan da suka same ni ba, har ma da sauran gidaje na da wuraren kasuwanci na, duk an kai hari a yau (Litinin), 23 ga Maris, 2026, daga jami’an da suka ce sun fito daga EFCC.”

EFCC
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa
EFCC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

MASU ALAKA

An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila
Manyan Labarai

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje
Labarai

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Next Post
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Yi Murabus

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Yi Murabus

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.