ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Ɗauki Matakin Ƙwace Wasu Gidajen Abubakar Malami A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
EFCC

Jami’an (EFCC) a jiya sun rufe gidajen tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami (SAN), da ke Abuja.

Hakan na zuwa ne yayin da (ICPC) ta sanar da shirin gurfanar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban kotu a yau kan zargin almundahanar kudade.

  • Saraki Ya Soki Gwamnatin Kwara Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro
  • Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

An ga wasu jami’an EFCC sanye da kayan farar hula suna sanya alama a gidajen Malami da ke Maitama, Abuja, a ranar Litinin, lamarin da ya jawo zanga-zanga daga bangaren tsohon AGF din, inda ya tambayi sahihancin takardun da jami’an suka gabatar.

ADVERTISEMENT

A yayin cacar baki da ta biyo baya, jami’an EFCC sun dage cewa takardun da suka kawo na umarnin kotu ne ingantattu, duk da korafin da Malami ya rika yi akai-akai.

“Ku nuna min inda aka ce ku zo ku kwace dukiyata… alhali shari’ar na gaban kotu, shin za ku iya yin hakan ba bisa ka’ida ba? Shin yana karkashin kwace dukiya ne bayan umarnin ya kare? Umarnin da aka bayar na kwanaki 14 ya riga ya kare, amma kuna zuwa ku kunyata ni.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Tun da sassafe kuna wani gidana, yanzu kuma kuna nan.

Ina umarnin da ya ba ku izinin zuwa kan dukiyata ku yi musu alama? Wannan umarnin nake son gani. Ku nuna min inda aka ce za ku iya zuwa ku yi alama a kan dukiyata. Prince (ya juya ga wani jami’in EFCC), ina umarnin? Umarnin nan ba ya bayyana a fili cewa kuna da izinin zuwa ku yi alama a kan dukiyata. Wannan lamari yana gaban kotu.

Ina umarnin kotu da ya ba ku izini? Shin kun zo ne don ku kunyata ni ba tare da dalili ba…? Ba tare da wani ingantaccen umarnin kotu ba, alhali shari’ar na gaban kotu, kuna zuwa kan dukiyata don ku kunyata ni. Haka ake yi ne? To, ku ci gaba ku yi alamar. Za mu hadu a kotu,” in ji Malami.

Sai dai an ji jami’in EFCC yana cewa, “Muna da ikon yin alama a kan dukiya idan tana karkashin dukiyar da za a kwace. Ga umarnin; na ba ka umarnin, ranka ya dade.”

A wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TB a ranar Litinin, Malami ya kara bayani kan rufe gidajensa, inda ya ce ya kalubalanci umarnin kotu da ke neman a yi kwacewar wucin gadi na dukiyoyinsa.

Ya ce, “Akwai jami’ai da suka zo sanye da kayan aiki cikakke, dauke da makamai, kuma sun kasance masu tsoratarwa da cin zarafi ga ‘yan uwana na kusa, har ma suna cewa sun zo ne don kai wasikun gayyata.

Daga karshe dai an bayar da wasikun, ba kawai a gidan da suka same ni ba, har ma da sauran gidaje na da wuraren kasuwanci na, duk an kai hari a yau (Litinin), 23 ga Maris, 2026, daga jami’an da suka ce sun fito daga EFCC.”

EFCC
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
EFCC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
  • Sulaiman
    Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026
  • Sulaiman
    Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Yi Murabus

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Yi Murabus

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.