ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Gurfanar Da Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 5.7

by Leadership Hausa
9 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) a ranar Talata ta gurfanar da Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi kuma tsohon manajan reshen bankin Polaris a Bauchi, Yakubu Adamu, a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite na babban Kotun tarayya da ke Maitama, Abuja bisa zarginsa da hannu wajen badaƙalar kuɗaɗe har N5,791,900,000.

 

ADVERTISEMENT

Adamu, an gurfanar da shi tare da kamfanin Ayab Agro Products da Freight Company Limited kan zarge-zargen guda shida da suka haɗa da sama da faɗi wanda ya saɓa wa sashi 21(a) da aka tanadar da hukunci bisa sashi 21 na dokar badaƙalar kuɗaɗe ta shekarar 2022.

  • An Yi Taron Ayyukan Noma Na Kwamitin Tsakiyar Kasar Sin A Beijing
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki a Janairu 1, 2026 — Tinubu

A lokacin da aka fara shari’ar, Lauyan masu shigar da ƙara, Samuel I. Chime, ya shaida wa kotu sun gabatar da ƙarar ne tare da roƙon a ba su damar su karanta ma wanda ake zargin tuhumar da ake masa.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Nemi Tinubu Ya Rage Farashin Man Fetur Don Sauƙaƙa Wa ’Yan Nijeriya Wahalar Da Suke Sha

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

 

Bayan karanta masa tuhume-tuhumensa, Yakubu Adamu ya ƙi amsa dukkanin zarge-zargen.

 

Ɗaya daga cikin zargin da ake yi wa Adamu shi ne, a lokacin da yake matsayin manajan reshen bankin Polaris da ke Bauchi a tsakanin watan Yuni zuwa Disamban 2023, ya haɗa baki da Ishaku Mohammed Aliyu, manajan gudanarwa na kamfanin I.S. Makayye Investment Resources Limited, da Muntaka Mohammed Duguri, waɗanda dukkanninsu a halin yanzu ake nemansu wajen sama da faɗi da Naira biliyan 4.65.

 

A cewar tuhumar, ta bankin Polaris aka saki kuɗaɗen da nufin sayo Babura wa gwamnatin jihar Bauchi ta hannun kamfanin Emmanuel Asomugha General Enterprises, amma ba a aiwatar da kwangilar sayo Baburan ba.

 

Kazalika, a wani tuhumar kuma, an zargi Yakubu Adamu da cewa a wani lokaci a shekarar 2023 ya tura Naira miliyan 976 zuwa asusun ajiyar kamfanin I.S. Makayye Investment Resources Limited, tare da sanin kuɗaɗen sun fito ta haramtaccen hanya da ke da alaƙa da karkatar da kayan banki.

 

Bayan da shi Adamu ya musanta cewa bai aikata laifukan ba, mai gabatar da ƙara ya roƙi a tsare wanda ake zargin har zuwa lokacin da zai nemi beli. Sai dai Lauyan kariya, Gordy Uche, SAN, ya gabatar da buƙatar neman belin wanda yake karewa, yayin da Lauyan da ke shigar da kara ya ƙi amincewa.

 

Bayan sauraron muhawarar kowane ɓangare, Mai Shari’a Nwite ya ware ranar 2 ga watan Janairun 2026 domin yanke hukunci kan buƙatar bayar da beli tare da bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake zargin a hannun EFCC.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar
  • Leadership Hausa
    Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari
  • Leadership Hausa
    Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

MASU ALAKA

Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba
Manyan Labarai

Atiku Ya Nemi Tinubu Ya Rage Farashin Man Fetur Don Sauƙaƙa Wa ’Yan Nijeriya Wahalar Da Suke Sha

September 18, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
Manyan Labarai

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

September 18, 2026
ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna
Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

September 18, 2026
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Shirin Inganta Lafiyar Yara Da Matasa Na Nan Zuwa Shekarar 2030

Sin Ta Gabatar Da Shirin Inganta Lafiyar Yara Da Matasa Na Nan Zuwa Shekarar 2030

LABARAI MASU NASABA

Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu

Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu

September 18, 2026
Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai

Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai

September 18, 2026
Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

Atiku Ya Nemi Tinubu Ya Rage Farashin Man Fetur Don Sauƙaƙa Wa ’Yan Nijeriya Wahalar Da Suke Sha

September 18, 2026
Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

September 18, 2026
Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

September 18, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

September 18, 2026
Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

September 18, 2026
Samun Ci Gaba Shi Ne Abu Mai Tushe Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam

Samun Ci Gaba Shi Ne Abu Mai Tushe Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam

September 18, 2026
Gwamnatin Najeriya Na Daukar Darasi Daga Salon Da Kasar Sin Ke Amfani Da Shi Na Kulla Alakar Diflomasiyya Ta Hanyar Jan Hankali Da Kyakkyawar Mu’amala

Gwamnatin Najeriya Na Daukar Darasi Daga Salon Da Kasar Sin Ke Amfani Da Shi Na Kulla Alakar Diflomasiyya Ta Hanyar Jan Hankali Da Kyakkyawar Mu’amala

September 18, 2026
ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

September 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.