ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Gurfanar Da Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 5.7

by Leadership Hausa
7 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) a ranar Talata ta gurfanar da Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi kuma tsohon manajan reshen bankin Polaris a Bauchi, Yakubu Adamu, a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite na babban Kotun tarayya da ke Maitama, Abuja bisa zarginsa da hannu wajen badaƙalar kuɗaɗe har N5,791,900,000.

 

ADVERTISEMENT

Adamu, an gurfanar da shi tare da kamfanin Ayab Agro Products da Freight Company Limited kan zarge-zargen guda shida da suka haɗa da sama da faɗi wanda ya saɓa wa sashi 21(a) da aka tanadar da hukunci bisa sashi 21 na dokar badaƙalar kuɗaɗe ta shekarar 2022.

  • An Yi Taron Ayyukan Noma Na Kwamitin Tsakiyar Kasar Sin A Beijing
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki a Janairu 1, 2026 — Tinubu

A lokacin da aka fara shari’ar, Lauyan masu shigar da ƙara, Samuel I. Chime, ya shaida wa kotu sun gabatar da ƙarar ne tare da roƙon a ba su damar su karanta ma wanda ake zargin tuhumar da ake masa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

 

Bayan karanta masa tuhume-tuhumensa, Yakubu Adamu ya ƙi amsa dukkanin zarge-zargen.

 

Ɗaya daga cikin zargin da ake yi wa Adamu shi ne, a lokacin da yake matsayin manajan reshen bankin Polaris da ke Bauchi a tsakanin watan Yuni zuwa Disamban 2023, ya haɗa baki da Ishaku Mohammed Aliyu, manajan gudanarwa na kamfanin I.S. Makayye Investment Resources Limited, da Muntaka Mohammed Duguri, waɗanda dukkanninsu a halin yanzu ake nemansu wajen sama da faɗi da Naira biliyan 4.65.

 

A cewar tuhumar, ta bankin Polaris aka saki kuɗaɗen da nufin sayo Babura wa gwamnatin jihar Bauchi ta hannun kamfanin Emmanuel Asomugha General Enterprises, amma ba a aiwatar da kwangilar sayo Baburan ba.

 

Kazalika, a wani tuhumar kuma, an zargi Yakubu Adamu da cewa a wani lokaci a shekarar 2023 ya tura Naira miliyan 976 zuwa asusun ajiyar kamfanin I.S. Makayye Investment Resources Limited, tare da sanin kuɗaɗen sun fito ta haramtaccen hanya da ke da alaƙa da karkatar da kayan banki.

 

Bayan da shi Adamu ya musanta cewa bai aikata laifukan ba, mai gabatar da ƙara ya roƙi a tsare wanda ake zargin har zuwa lokacin da zai nemi beli. Sai dai Lauyan kariya, Gordy Uche, SAN, ya gabatar da buƙatar neman belin wanda yake karewa, yayin da Lauyan da ke shigar da kara ya ƙi amincewa.

 

Bayan sauraron muhawarar kowane ɓangare, Mai Shari’a Nwite ya ware ranar 2 ga watan Janairun 2026 domin yanke hukunci kan buƙatar bayar da beli tare da bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake zargin a hannun EFCC.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Shirin Inganta Lafiyar Yara Da Matasa Na Nan Zuwa Shekarar 2030

Sin Ta Gabatar Da Shirin Inganta Lafiyar Yara Da Matasa Na Nan Zuwa Shekarar 2030

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.