ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Gurfanar Da Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 5.7

by Leadership Hausa
6 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) a ranar Talata ta gurfanar da Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi kuma tsohon manajan reshen bankin Polaris a Bauchi, Yakubu Adamu, a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite na babban Kotun tarayya da ke Maitama, Abuja bisa zarginsa da hannu wajen badaƙalar kuɗaɗe har N5,791,900,000.

 

ADVERTISEMENT

Adamu, an gurfanar da shi tare da kamfanin Ayab Agro Products da Freight Company Limited kan zarge-zargen guda shida da suka haɗa da sama da faɗi wanda ya saɓa wa sashi 21(a) da aka tanadar da hukunci bisa sashi 21 na dokar badaƙalar kuɗaɗe ta shekarar 2022.

  • An Yi Taron Ayyukan Noma Na Kwamitin Tsakiyar Kasar Sin A Beijing
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki a Janairu 1, 2026 — Tinubu

A lokacin da aka fara shari’ar, Lauyan masu shigar da ƙara, Samuel I. Chime, ya shaida wa kotu sun gabatar da ƙarar ne tare da roƙon a ba su damar su karanta ma wanda ake zargin tuhumar da ake masa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

 

Bayan karanta masa tuhume-tuhumensa, Yakubu Adamu ya ƙi amsa dukkanin zarge-zargen.

 

Ɗaya daga cikin zargin da ake yi wa Adamu shi ne, a lokacin da yake matsayin manajan reshen bankin Polaris da ke Bauchi a tsakanin watan Yuni zuwa Disamban 2023, ya haɗa baki da Ishaku Mohammed Aliyu, manajan gudanarwa na kamfanin I.S. Makayye Investment Resources Limited, da Muntaka Mohammed Duguri, waɗanda dukkanninsu a halin yanzu ake nemansu wajen sama da faɗi da Naira biliyan 4.65.

 

A cewar tuhumar, ta bankin Polaris aka saki kuɗaɗen da nufin sayo Babura wa gwamnatin jihar Bauchi ta hannun kamfanin Emmanuel Asomugha General Enterprises, amma ba a aiwatar da kwangilar sayo Baburan ba.

 

Kazalika, a wani tuhumar kuma, an zargi Yakubu Adamu da cewa a wani lokaci a shekarar 2023 ya tura Naira miliyan 976 zuwa asusun ajiyar kamfanin I.S. Makayye Investment Resources Limited, tare da sanin kuɗaɗen sun fito ta haramtaccen hanya da ke da alaƙa da karkatar da kayan banki.

 

Bayan da shi Adamu ya musanta cewa bai aikata laifukan ba, mai gabatar da ƙara ya roƙi a tsare wanda ake zargin har zuwa lokacin da zai nemi beli. Sai dai Lauyan kariya, Gordy Uche, SAN, ya gabatar da buƙatar neman belin wanda yake karewa, yayin da Lauyan da ke shigar da kara ya ƙi amincewa.

 

Bayan sauraron muhawarar kowane ɓangare, Mai Shari’a Nwite ya ware ranar 2 ga watan Janairun 2026 domin yanke hukunci kan buƙatar bayar da beli tare da bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake zargin a hannun EFCC.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Shirin Inganta Lafiyar Yara Da Matasa Na Nan Zuwa Shekarar 2030

Sin Ta Gabatar Da Shirin Inganta Lafiyar Yara Da Matasa Na Nan Zuwa Shekarar 2030

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.