A yau Litinin ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya gana da firaminista, kana ministan harkokin wajen kasar Qatar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani a nan birnin Beijing.
Yayin zantawarsu, Li ya ce a Gabas ta Tsakiya da yankin Gulf, Qatar muhimmiyar kawa ce ta Sin bisa manyan tsare-tsare, kuma Sin ta shirya yin aiki tare da Qatar, wajen kara inganta tuntuba da tsare-tsare, kana sassan biyu suna goyon bayan juna a muhimman batutuwan da suke jan hankalinsu, tare da ingiza dangantakarsu, ta yadda za su kai ga amfanar da al’ummunsu.
Kazalika, firaministan na Sin ya ce kasarsa na goyon bayan yunkurin shiga tsakani da Qatar ke yi a batutuwan Gabas ta Tsakiya, ta kuma shirya yin aiki tare da Qatar, da sauran kasashen shiyyar, da ma sauran sassan kasa da kasa, ta yadda za a kai ga gaggauta dawo da zaman lafiya da walwala a shiyyar.
A nasa bangare kuwa, Al Thani, cewa ya yi Qatar na martaba alakarta da Sin, kuma kasashen biyu suna ci gaba da ingiza amincewa juna, da martaba juna, da cimma moriya tare da samun nasarorin bai daya.
Ya ce Qatar na godiya da jinjinawa kokarin kasar Sin a fannin goyon bayan zaman lafiya, da daidaito a Gabas ta Tsakiya, kuma ta himmatu wajen ganin an warware rigingimu ta hanyar tattaunawa da dawo da zaman lafiya a yankin. (Saminu Alhassan)














