• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Kungiyoyin Sun Bukaci Buhari Da APC Su Zabi Boss Mustapha A Mataimakin Tinubu

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
Gamayyar Kungiyoyin Sun Bukaci Buhari Da APC Su Zabi Boss Mustapha A Mataimakin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar kungiyoyin rajin kare hakkin dimokradiyya da fararen hula, sun roki shugaban kasa, Muhammadu Buhari da jam’iyyar APC da su amince da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bai wa jam’iyyun siyasa wa’adin zuwa ranar Juma’a 17 ga watan Yunin 2022 da su mika sunayen ‘yan takararsu na shugaban kasa da mataimakinsa ga hukumar.

  • 2023: Wasu ‘Yan Jam’iyyar APC Sun Nemi Tinubu Ya Dauki Gwamnan Neja Mataimaki
  • 2023: Ban Ce Zan Dauki Mataimaki Musulmi Ba – Tinubu

A wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba, gamayyar kungiyoyin da suka hada da kungiyar kare hakkin ‘yan asalin kasa (PAIR) da Civil Society Action for National Inclusion (CSANI), da Society for Equity and Gender Advocacy (SEGA), sun ce, Mustapha ya yi fice a cikin duk wasu da ake yi wa hasashen basu mataimakin.

“Boss Mustapha mai rikon amana ne kuma ba shi da wata hayaniya ko wani cikas da zai durkusar da shirin APC na ci gaba da rike madafun iko a 2023,”

“A matsayinsa na Kiristan Arewa, mustapha zai dace da ma’aunin da ake bukata, tare da rage fargaba a wurin al’umar Kirista. da kuma tabbatar da cewa za a kare muradun Arewa,” in ji kungiyar.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

A cikin sanarwar da Isa Pai, Chukwudi Emmanuel da Fola Akin suka sanya wa hannu, sun bayyana cewa, “a tsawon shekaru, Boss Mustapha, sakataren gwamnatin tarayya ya nuna kwazo a cikin ayyukansa, jajircewa da kuma biyayya ga manufofin shugaban kasa Muhammadu. Buhari.

“A matsayinsa na shugaban kwamitin shugaban kasa kan COVID-19, Boss Mustapha ya nuna cewa yana iya aiwatar da lamuran da Suka shafi kasa cikin gaggawa, abin da ake bukata shi ne mutumin da zai iya jagoranci, tsarawa, kai tsaye da mayar da hankali.”

Don haka kungiyar ta yi kira ga “Shugaba Muhammadu Buhari da shugabannin jam’iyyar APC da su aiwatar kamar yadda suka saba yi.

“Yayin da gaba ta karshe ko gab da kammala zaben dan takarar mataimakin shugaban kasa, Boss Mustapha ya fi kowa dacewa a halin yanzu ta fuskar tarihinsa mara lahani, aikin gwamnati da kasa, alkibla da manufa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBoss MustaphaBuhariKungiyoyiMataimakin Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

Next Post

‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

Related

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

2 days ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

3 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

6 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

6 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

6 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

6 days ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

LABARAI MASU NASABA

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.