A Jihar Ribas, rikicin siyasa ya ɗauki sabon salo bayan ƴan majalisar dokoki su 16, ciki har da Kakakin Majalisar Martin Amaewhule, sun sanar da ficewarsu daga PDP zuwa APC. Wannan mataki ya bayyana ne a zaman majalisar da aka gudanar ranar Juma’a, wanda ya sake kunna rikicin siyasar da ke tsakanin Ministan FCT Nyesom Wike da Gwamna Siminalayi Fubara.
Kakakin Majalisar, Martin Amaewhule, ya ce sun yanke shawarar barin PDP ne saboda jam’iyyar ta rabu biyu kuma ta gaza wakiltar abin da suka tsaya a kai. Ya kara da cewa matsin lamba da rashin daidaito a cikin jam’iyyar ya sa suka ga dacewar sauya sheƙa gaba ɗaya zuwa APC domin ci gaba da wakiltar jama’arsu cikin kwanciyar hankali.
- Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
- Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
Sauyin ya jawo girgiza a siyasar Jihar Ribas, kasancewar PDP ta daɗe tana da rinjaye a majalisar. Ficewar ƴan majalisar 16 ɗin na nufin APC za ta samu ƙarfi sosai a zauren majalisa, abin da ka iya sauya tsari da tasirin mulkin jihar nan gaba kaɗan.
Masu nazarin siyasa na ganin wannan sauyi wani babban koma baya ne ga jam’iyyar PDP a Ribas tare da yiwuwar ƙara tsananta rikicin siyasar da ya jima yana ci tsakanin manyan ɓangarori biyu a jihar. Duk da haka, ana sa ran matakin zai sake fayyace tasirin kowanne ɓangare yayin da rikicin ke ƙara zafafa.














