ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Bukola Saraki Za Ta Fara Raba Abincin Buɗe Baki Daga Gobe

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Bukola

Gidauniyar Dr. Abubakar Bukola Saraki za ta fara raba dafaffen abinci ga masu azumi a lokacin shan ruwa wanda ta saba yi duk shekara a jihohi bakwai da babban birnin tarayya Abuja.

Rabon abincin wanda ake yi a kwanaki goma na ƙarshe na watan azumin Ramadan yana cikin ayyukan da gidauniyar take yi na tallafawa marasa a ƙarfi a cikin al’umma.

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Bukola Saraki Ya Je Bauchi Ta’aziyyar Ɗahiru Bauchi

Wannan shirin wanda aka jima ana yi, yana ɗaya daga cikin shirye-shiryen da gidauniyar take yi a duk lokacin azumi domin tallafawa marasa ƙarfi musamman masu yin azumi tare kuma da tabbatar da ganin cewa al’umma suna buɗa baki da abinci mai gina jiki.

ADVERTISEMENT

Ciyarwar wannan shekarar za ta gudana ne a jihohin Neja da Sokoto da Bauchi da Borno da Kaduna da Plateau da babban birnin tarayya Abuja, inda ake raba abinci dafaffe a masallatai guda biyu a kowace jiha kuma mutane 100 ne suke amfana da abincin a kullum a kowane masallaci.

A jihar Kwara, inda gidauniyar ta daɗe tana raba abincin a gaba ɗaya faɗin jihar za a raba abincin ne a masallatai daban-daban har guda 52.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Da yake magana gabanin fara rabon abincin, babban daraktan gidauniyar, Dr. Audu Idowu Musa ya ce watan azumi yana bawa masu hannu da shuni dama domin su taimaki mutane tare da sake samun kusanci ga al’umma.

“A irin wannan lokacin al’umma suna tsananin buƙatar taimako musamman magidanta, saboda halin da tattalin arzikin ƙasa yake ciki, samun abinci yana da wahala sosai kuma kowa yana ji a jikinsa ‘ in ji Dr. Audu

Ya ci gaba da cewa “mutane musamman masu ƙaramin ƙarfi suna buƙatar agaji. Saboda haka wannan lokacin shi ne lokacin da ya kamata a taimaki al’umma. Bugu da ƙari taimakawa mutane yana nuna cewa har yanzu akwai mutanen da suka damu da halin da marasa ƙarfi suke ciki a wannan lokacin da rayuwa ta yi tsada.’

Ya ƙara da cewa ciyarwa a cikin azumi ya nuna irin yadda gidauniyar ta saka walwalar al’umma a gaba musamman masu rauni. Shekara da shekaru gidauniyar Abubakar Bukola Saraki tana ayyukan jinƙai, tallafin karatu da lafiya da ci gaban al’umma, kuma wannan ciyarwar tana ɗaya daga ciki.

Gidauniya ta ce waɗanda za su taimaka wajen gudanar da raba abincin da shugabannin al’umma da limamai tuni sun gama shiri wajen ganin komai ya tafi yadda aka tsara.

Gidauniyar ta kuma yi kira ga al’umma da su yi amfani da wannan watan wajen yin addu’ar zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a Najeriya.

Bukola
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.