ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Bukola Saraki Za Ta Fara Raba Abincin Buɗe Baki Daga Gobe

by Abba Ibrahim Wada
3 months ago
Bukola

Gidauniyar Dr. Abubakar Bukola Saraki za ta fara raba dafaffen abinci ga masu azumi a lokacin shan ruwa wanda ta saba yi duk shekara a jihohi bakwai da babban birnin tarayya Abuja.

Rabon abincin wanda ake yi a kwanaki goma na ƙarshe na watan azumin Ramadan yana cikin ayyukan da gidauniyar take yi na tallafawa marasa a ƙarfi a cikin al’umma.

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Bukola Saraki Ya Je Bauchi Ta’aziyyar Ɗahiru Bauchi

Wannan shirin wanda aka jima ana yi, yana ɗaya daga cikin shirye-shiryen da gidauniyar take yi a duk lokacin azumi domin tallafawa marasa ƙarfi musamman masu yin azumi tare kuma da tabbatar da ganin cewa al’umma suna buɗa baki da abinci mai gina jiki.

ADVERTISEMENT

Ciyarwar wannan shekarar za ta gudana ne a jihohin Neja da Sokoto da Bauchi da Borno da Kaduna da Plateau da babban birnin tarayya Abuja, inda ake raba abinci dafaffe a masallatai guda biyu a kowace jiha kuma mutane 100 ne suke amfana da abincin a kullum a kowane masallaci.

A jihar Kwara, inda gidauniyar ta daɗe tana raba abincin a gaba ɗaya faɗin jihar za a raba abincin ne a masallatai daban-daban har guda 52.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Da yake magana gabanin fara rabon abincin, babban daraktan gidauniyar, Dr. Audu Idowu Musa ya ce watan azumi yana bawa masu hannu da shuni dama domin su taimaki mutane tare da sake samun kusanci ga al’umma.

“A irin wannan lokacin al’umma suna tsananin buƙatar taimako musamman magidanta, saboda halin da tattalin arzikin ƙasa yake ciki, samun abinci yana da wahala sosai kuma kowa yana ji a jikinsa ‘ in ji Dr. Audu

Ya ci gaba da cewa “mutane musamman masu ƙaramin ƙarfi suna buƙatar agaji. Saboda haka wannan lokacin shi ne lokacin da ya kamata a taimaki al’umma. Bugu da ƙari taimakawa mutane yana nuna cewa har yanzu akwai mutanen da suka damu da halin da marasa ƙarfi suke ciki a wannan lokacin da rayuwa ta yi tsada.’

Ya ƙara da cewa ciyarwa a cikin azumi ya nuna irin yadda gidauniyar ta saka walwalar al’umma a gaba musamman masu rauni. Shekara da shekaru gidauniyar Abubakar Bukola Saraki tana ayyukan jinƙai, tallafin karatu da lafiya da ci gaban al’umma, kuma wannan ciyarwar tana ɗaya daga ciki.

Gidauniya ta ce waɗanda za su taimaka wajen gudanar da raba abincin da shugabannin al’umma da limamai tuni sun gama shiri wajen ganin komai ya tafi yadda aka tsara.

Gidauniyar ta kuma yi kira ga al’umma da su yi amfani da wannan watan wajen yin addu’ar zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a Najeriya.

Bukola
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.