ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Bukola Saraki Za Ta Fara Raba Abincin Buɗe Baki Daga Gobe

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Bukola

Gidauniyar Dr. Abubakar Bukola Saraki za ta fara raba dafaffen abinci ga masu azumi a lokacin shan ruwa wanda ta saba yi duk shekara a jihohi bakwai da babban birnin tarayya Abuja.

Rabon abincin wanda ake yi a kwanaki goma na ƙarshe na watan azumin Ramadan yana cikin ayyukan da gidauniyar take yi na tallafawa marasa a ƙarfi a cikin al’umma.

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Bukola Saraki Ya Je Bauchi Ta’aziyyar Ɗahiru Bauchi

Wannan shirin wanda aka jima ana yi, yana ɗaya daga cikin shirye-shiryen da gidauniyar take yi a duk lokacin azumi domin tallafawa marasa ƙarfi musamman masu yin azumi tare kuma da tabbatar da ganin cewa al’umma suna buɗa baki da abinci mai gina jiki.

ADVERTISEMENT

Ciyarwar wannan shekarar za ta gudana ne a jihohin Neja da Sokoto da Bauchi da Borno da Kaduna da Plateau da babban birnin tarayya Abuja, inda ake raba abinci dafaffe a masallatai guda biyu a kowace jiha kuma mutane 100 ne suke amfana da abincin a kullum a kowane masallaci.

A jihar Kwara, inda gidauniyar ta daɗe tana raba abincin a gaba ɗaya faɗin jihar za a raba abincin ne a masallatai daban-daban har guda 52.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Da yake magana gabanin fara rabon abincin, babban daraktan gidauniyar, Dr. Audu Idowu Musa ya ce watan azumi yana bawa masu hannu da shuni dama domin su taimaki mutane tare da sake samun kusanci ga al’umma.

“A irin wannan lokacin al’umma suna tsananin buƙatar taimako musamman magidanta, saboda halin da tattalin arzikin ƙasa yake ciki, samun abinci yana da wahala sosai kuma kowa yana ji a jikinsa ‘ in ji Dr. Audu

Ya ci gaba da cewa “mutane musamman masu ƙaramin ƙarfi suna buƙatar agaji. Saboda haka wannan lokacin shi ne lokacin da ya kamata a taimaki al’umma. Bugu da ƙari taimakawa mutane yana nuna cewa har yanzu akwai mutanen da suka damu da halin da marasa ƙarfi suke ciki a wannan lokacin da rayuwa ta yi tsada.’

Ya ƙara da cewa ciyarwa a cikin azumi ya nuna irin yadda gidauniyar ta saka walwalar al’umma a gaba musamman masu rauni. Shekara da shekaru gidauniyar Abubakar Bukola Saraki tana ayyukan jinƙai, tallafin karatu da lafiya da ci gaban al’umma, kuma wannan ciyarwar tana ɗaya daga ciki.

Gidauniya ta ce waɗanda za su taimaka wajen gudanar da raba abincin da shugabannin al’umma da limamai tuni sun gama shiri wajen ganin komai ya tafi yadda aka tsara.

Gidauniyar ta kuma yi kira ga al’umma da su yi amfani da wannan watan wajen yin addu’ar zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a Najeriya.

Bukola
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.