ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (5)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
Manzon Allah

‘Yan’uwa assalamu alaikum warahmtullahi ta’ala wa barkatuhu. Har yanzu dai muna nan a cikin bayanin rantsuwar da Allah ya yi da darajojin shugaban halitta, Annabi Muhammad (SAW) inda a makon jiya muka kwana a bayani kan abubuwan da muke imani da su ba tare da dora wa kanmu cewa dole sai mun gano abin ba. Kuduri ne kawai za mu yi sai mu yi imani a zuciya.

Haka nan zaman Arfa, wani wuri ne muke zuwa mu zauna kawai, a nan za mu yi Sallar Azahar da La’asar amma kuma ba a so mu yi Sallar Magriba da Isha’i a wurin don ma kar mu zaci ko wannan ne silar da ta sa aka ce mu je wurin, dole sai mun tafi Muzdalifa kafin mu karasa sauran sallolin.

  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3
  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin

Abin da ake so kawai mu je Arfa mu zauna kuma wannan zaman shi ne Hajji baki daya kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya ce, “Arfa ita ce Hajji”.

ADVERTISEMENT

Ka ga duk a rin wannan sai dai bin umurni ne kawai, walau mun gane hikimar da ke ciki ko ba mu gane ba. Ba kowane Musulmi ne zai ce ya san duk dalilan da Allah ya ce a yi wadannan ibadun ba, don haka ko mutum ya gane ko bai gane ba ya aikata kawai saboda dalilin cewa Allah ne ya umurci a yi. Kamar dai yadda soja yake, idan ya ba da umurni ba za a tsaya tambayar dalili ba, za a aikata ne kawai sai in daga baya tukuna bayan an gama sai a tambaya. Saboda haka a cikin aikin ibadu da aka ce mu yi, ba sai mun san dalili ba, mu Allah muke bi, tunda ya ce a yi, mu aikata kawai ko mun san dalilin ko ba mu sani ba.

Haka nan ko a cikin kudurcewar ma akwai abin da mun yi imani da shi, ko mun iya ganewa ko ba mu iya ba. Manzon Allah (SAW) ya ba mu labari daga Allah ne kuma mun yarda mun yi imani da shi kamar mun gani. Misali, Manzon Allah ya ba mu labarin akwai wata irin gada a lahira sunanta Siradi, a kan wuta za a shimfida ta, ta fi silin gashi siriri, ta fi takobi kaifi, kuma duk halitta za ta bi ta kanta, wannan gada kuwa wace iri ce? Amma kuma lallai mun yarda akwai ta mun yi imani da ita. Duk wanda bai yi imani da ita ba sai Shari’a ta caje shi da laifin rashin imani. To irin wannan imani ne kawai ake kudurcewa a zuciya. Kamar yadda labarin gadar nan ta Siradi take, haka ma akwai wasu maganganun Allah a cikin Alkur’ani da ya saukar wanda sai dai imani kawai, amma ba mu san ma’anarsu ba. Yana daga cikinsu wadannan rantsuwa da Allah ya yi da Alif Lam Miym. Malamai masu Tafsiri karshen abin da suke fassarawa da shi shi ne “Allah ne ya fi sanin abin da yake nufi da wannan”. Sai dai, Malaman da Allah ya haskaka musu sukan yi tawili kawai. Ma’anar tawili kamar mu a Hausa, wani ya zo ya ce “wane ya ci mun mutunci”, ma’anarsa ya bata masa suna. Ko a ce “wane ya yi mun yankan kauna”, ma’anar zancen shi ne mutum ya zaci zai iya sa wani ya aikata wani abu ko ya hana shi amma sai ya ki. A nan duk, maganganun da aka fada a zahiri sun saba da ma’anoninsu na ainihi. Wasu masana kuma za su iya fassara wadannan zantukan da wani abu daban. Kamar misali, idan aka ce “wane ya yi mun cin mutunci” ana nufin an kawo abinci ga wani mutum (kamar bako) sai ya ci dan kadan ya ce ruwa kawai yake so, to a nan sai a ce ya yi cin mutunci. Ko kuma idan aka ga yara suna cin abinci suna wawaso sai a ce “kai ku bari; ku yi cin mutunci”. A bangaren “Yankan kauna” kuma, a wata fassarar kamar a ce mutum ne ya sayi ragonsa na sunan jaririn da matarsa ta haifa, kawai sai ya yi bako kafin ranar sunan sai ya umurci a yanka wa bakon nan ragon, a nan sai a ce “wane ya yi mun yankan kauna”. Duk wadannan suna da ma’anarsu da ta fito a zahiri mutane suka san ta; sannan suna da ma’anarsu da ta dan buya sai masanan abin za su bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

Kamar yadda misalin Hausa nan yake, haka nan karatun da muke karantawa ma’anarsa take. Fassarar zahirin tana nan amma kuma akwai malaman da Allah ya haskaka musu suka fahimci wata ma’anar daban, kamar yadda wasu suka riki cin mutunci ba a matsayin zagi ba ko yankan kauna a matsayin kunyatawa.

To Allah (SWT) a cikin rantse-rantsen nasa, akwai wadda ya yi da harafi akwai kuma wadda ya yi da kalma. Kamar su “Saad”, “Kaaf”, “Nuun”, duka wadannan haruffa ne dai-dai. Na kalmomi kuma su ne kamar “Wannajmi”, “Wal’asri” da sauran su. Sannan Allah ya yi rantsuwa da haruffa biyu-biyu irin su “He miym”, “Da ha”, haka nan da kalma biyu-biyu kamar “Wadduhe. Wallaili izha saje”, “wassama’i waddarik”. Sai kuma rantsuwa da harafi uku-uku, kamar “Alif Lam Miym” da muka yi bayani a sama. Na kalmomi uku kuma kamar ayoyin ukun farkon Suratus Saafaat. Akwai wuraren da Allah ya rantse da haruffai hudu-hudu, kamar “Alif Lam Miym Saad” da kuma wurin da ya rantse da kalmomi hudu kamar ayoyi hudun farkon Suratuz Zariyati. Har ila yau, akwai inda Allah ya rantse da haruffa guda biyar, kamar “Kaaf Haa Yaa Ain Saad” da “He miym Ain Siyn Kaaf”, sannan akwai na kalmomi biyar kamar daga “wadduur wa kitaabin masduur…” ko “Walmursalati urfa fal’asifaati asfa… “Wannazi’ati garka wannashidaati nashda….” har zuwa kan na biyar-biyar din ayoyin. Gaba dayan rantse-rantsen su 28 ne, kuma ikon Allah, Allah ya raba su rabi-rabi, na haruffa sau 14; na kalma ma sau 14. Na kalmomi ana sanin ma’anarsa amma na haruffa sai dai a ce “Allah ne mafi sanin abin da yake nufi da su”. Amma kuma ga Sahabbai da sauran Waliyyan Allah sun fadi ma’anarsu kamar yadda Allah ya haska musu tawilinsu wanda idan mutum ya dauka sai ya amfanu kuma ya amfanar.

Manzon Allah
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

MASU ALAKA

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
Dausayin Musulunci

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

June 12, 2026
Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.