Wata mummunar gobara ta lalata shaguna da dama a shahararriyar Kasuwar Mandate da ke Ilorin, babban birnin Jihar Kwara.
Lamarin, wanda ya faru da sanyin safiyar ranar Talata, ya jefa ‘yan kasuwar cikin rudani da firgici.
Rahotanni sun nuna cewa ‘yan kasuwa da mazauna yankin sun yi ƙoƙarin kashe wutar kafin isowar jami’an kashe gobara.
Gobarar ta ƙone shaguna da kayayyaki na miliyoyin nairori.
Da yake magana kan lamarin, Babalolan Kasuwar Mandate, Alhaji Murtala Tambaruku, ya shaida wa Daily Trust cewa, ‘yan kasuwar sun yi asarar dukiyoyi na miliyoyin naira sakamakon gobarar.
A cewarsa, da dama daga cikin waɗanda abin ya shafa sun shiga cikin matsanancin damuwa, inda wasu ma suka suma bayan ganin irin barnar da gobarar ta yi.















Discussion about this post