ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
Ramadan

Goman ƙarshen Ramadan su ne mafi girman dararen duniya baki ɗaya, domin a cikinsu Lailatul-Ƙadari yake. Allah Ta’ala Yana cewa: “Lailatul-Ƙadari ya fi wata dubu alheri” Suratul Ƙadri aya ta 3.

Babban malamin tafsiri al-Imam al-Bagawi, Allah Ya yi masa rahama yana cewa: “Malaman tafsiri sun bayyana ma’anar ayar da cewa: aikata aikin ƙwarai a cikin daren Lailatul-Ƙadari shi ne ya fi alheri sama da aikin ƙwarai a cikin watanni dubu wanda babu Lailatul-Ƙadari a cikinsu”

  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Hadisi ya tabbata a cikin Al-mujtaba na Imam an-Nasa’i da Musnad na Imam Ahmad daga Abu Huraira Allah Ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ramadana ya zo muku, wata ne mai wata irin albrka, Allah Mai girma da ɗaukaka ya wajabta muku azumtar sa, ana buɗe ƙofofin Aljanna a cikinsa, ana kuma rufe ƙofofin Jahannama a cikinsa, a cikinsa akwai wani dare da ya fi wata dubu alheri, duk wanda aka haramta masa alherinsa, to, tabbas an haramta masa alheri”

ADVERTISEMENT

Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk wanda ya tsayu a daren Lailatul-Ƙadari yana mai imani da neman lada, to, an gafarta masa zunubansa”

Wannan dare yana cikin goman ƙarshe na Ramadan. Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana cewa da Sahabbai: Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a goman ƙarshe na Ramadan. Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

LABARAI MASU NASABA

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Ana karɓo hadisi daga Nana Aishatu, Allah Ya ƙara yarda a gare ta, ta ce: Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a cikin dare mara na goman ƙarshe na Ramadana” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Manzon Allah (S.AW) ya fi kowa girman matsayi da alfarma da daraja da martaba a wurin Allah. Allah Ya gafarta masa abin da ya aikata da wanda bai aikata ba amma duk da haka yana ƙara ƙaimi da ƙwazo a goman ƙarshe na Ramadan sama da ƙwazonsa a goman farko da ta tsakiya na wannan wata mai albarka. Nana Aisha Allah Ya ƙara mata yarda ta ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan goman ƙarshe ta shiga, sai ya ƙara zage dantse, ya kuma raya daren gaba ɗaya, kuma ya tayar da iyalansa daga barci” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito. A wata ruwaya ta Muslim cewa ta yi:” Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana ƙoƙari a goman ƙarshe irin ƙoƙarin da baya yinsa a waninsa”

Sayyadina Aliyu ɗan Abu Ɗalib, Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: “Lalle annabi (S.A.W) ya kasance yana tayar da iyalansa a goman ƙarshe na Ramadana” Tirmizi ne ya ruwaito da salsala ingantacciya.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Next Post
Isra’ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

Isra'ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.