Ƙungiyar malaman jami’o’i (ASUU), ta yi barazanar shiga yajin aiki na dindindin a jami’o’in jihohi 11, idan gwamnatocin jihohin Ido, Delta, Ondo, Adamawa, Borno, Taraba da Yobe suka kasa aiwatar da yarjejeniyar gwamnatin tarayya da ASUU daga nan zuwa ƙarshen watan Yuli na shekarar 2025.
Shiyyoyin Benin da Yola na ƙungiyar, sun yi wannan gargaɗin ne a wani taron manema labarai daban-daban a ranar Litinin, inda suka zargi gwamnatocin jihohin da abin ya shafa da gaza aiwatar da yarjejeniyar wata shida, bayan ƙulla yarjejeniyar.
Shugaban shiyyar Benin, Farfesa Monday Igbafen, ya ce; rassan ASUU da ke cikin jami’o’in da abin ya shafa, sun fara haɗa kan mambobin ƙungiyar, domin rufe harkokin ilimi baki-ɗaya.
Jami’o’in, sun haɗa da Jami’ar Ambrose Alli, Ekpoma; Adekunle Ajasin, Akungba-Akoko; Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Olusegun Agagu, Okitipupa; Jami’ar Jihar Delta, Abraka; Jami’ar Delta, Agbor; Jami’ar Dennis Osadebay, Asaba; Jami’ar Kudancin Delta, Ozoro; Jami’ar Jihar Adamawa, Mubi; Jami’ar Jihar Borno, Maiduguri; Jami’ar Jihar Taraba, Jalingo; da kuma Jami’ar Jihar Yobe, Damaturu.
Igbafen ya ce, yayin da jami’o’in gwamnatin tarayya da jami’o’in jihohi da dama suka aiwatar da yarjejeniyar, har yanzu jihohin da abin ya shafa ba su biya kuɗin tallafin karatu na CATA da sauran alawus-alawus da basussukan da aka amince da su daga watan Janairun 2026.
Haka zalika, Shugaban shiyyar Yola, Kwamared Dani Mamman, ya ce; ci gaba da rashin aiwatar da yarjejeniyar da sauran alawus-alawus ɗin da aka tattauna, ya haifar da tashin hankali a cibiyoyin da abin ya shafa.
Har ila yau, ya kuma bayyana lamarin a matsayin rashin adalci da kuma keta haddi na gamayya, yana mai jaddada cewa; malamai suna neman halak ɗinsu ne kawai.
Ƙungiyar ta yi kira ga gwamnonin da abin ya shafa, da su gaggauta aiwatar da yarjejeniyar tare da warware duk wasu basussukan da ake bin su, domin kaucewa yajin aikin da ba a san ƙarshensa ba, wanda ka iya harfar da koma baya a sha’anin ilimi.














