Jama’a barkanmu da juma’a barkanmu da sake kasancewa tare da wannan shafin na GORON JUMA’A, shafin da ke bawa kowa damar mika sakon gaishe-gaishensa zuwa ga ‘yan’uwa da abokan arziki na kusa da na nesa har ma da wadanda aka dade ba a hadu ba.
Kamar kowane mako yau ma shafin na dauke da wasu sakonnin gaishe-gaishen da ku ka aiko mana, inda sakon farko ya fara da cewa:
Sako daga Nafisah Muhammad Isah Mina Jihar Niger:
Ina gaishe da ‘yan’uwana kamar su Aisha Muhammad Isah (Ayushatee), Muhammad Muhammad Isah Mina, Dawud Muhammad Isah Mina, da sauransu, sai kawayena na makanta da malamaina. Da fatan za su yi sallar juma’a lafiya, Amin.
Sako daga Fatiyya Jibril Isah Jihar Kaduna:
Ina gaishe da Uwar dakina kuma Uwata a gurin Sana’a wato Hajiyya Aisha mai abinci. Sannan kawata kuma aminiyata wato Shamsiyya, sai ‘yan’uwana na gida kamar su Hajja Uwani mai Alala, sai Mardiyya, Zulai da dai sauransu. Sai ‘yan’uwana dake Kano da Maiduguri da fatan sun yi sallar juma’a lafiya.
Sako daga Hamisu Bala Dagaci daga Jihar Kano:
Da farko ina mika sakon goron juma’ata zuwa ga daukacin jama’a musulmi barka da juma’a, sai ‘yan’uwana na kusa da na nesa da abokan arziki, makofta da dai sauransu kamar Alhaji Mamman Shitu, Yusha’u Garba Danlami, Jamilu Mahummad.
Sunana Fatima Muhammad Hashim daga Jihar Kaduna:
Ina gaishe da Mamana da Babana, sai yayata dake garin Kano wato Yaya Hajiya, sai Yaya Muhammad dayake karatu a Katsina. Sai kawayena na makaranta Suwaibah Muhammad, Hajara, Zauwariyya, Zaina Abdulmajeed, Rukayya Abdullahi, Kausar Nuhu, Fatima Suleiman, Aisha Hafizu, da dai sauransu. Da fatan sun yi juma’a lafiyya, Amin.
Sako daga Maimunatu Aliyu Minjibir jihar Kano:
Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai ‘Yata Mariya, da kannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.













