Shugabar babban asibitin Sheikh Muhammad Jidda, Dakta Fatima Ibrahim Hamza ta bayyana cewa yanzu haka Gwamna Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, a ƙoƙarinsa na inganta harkokin lafiya ya sabanta asibitin Sheikh Muhammad Jidda da aka fi sani da suna asibitin Kuroda da ke Birnin Kano.
Ta ce duk wanda ya ziyarci wannan asibiti domin neman lafiya ko gaida mara lafiya zai zama shaidar gani da ido, wannan ci gaban da aka samu Kano a fannin lafiya ya samo asali daga yadda Gwamna Abba ya zaɓo kwamishinan lafiya, Dakta Abubakar Labaran Yusuf da shugaban hukumar kula da asibitocin Kano. Dakta Mansur Nagoda da sauran masu ruwa da tsaki da gwamna ya naɗa kuma suke jajircewa.
Dakta Fatima ta bayyana haka ne a lokacin da take ƙarin bayani kan ci gaban da gwamna ya kawo a cikin shekara uku da hawansa mulki.Ta ƙara da cewa a fannin kayan aiki da magunguna na shirin ‘Saɓatta Juyatta’ wato shirin da ya tanadar da samar da magunguna daga hukumar DMCSA, wanda a yanzu mara lafiya kan samu magani a ƙalla kashi 9 cikin 10, cikin sauƙi da inganci.
Haka kuma ta ce akwai gine-gine da asibitin ya samu da wuraran zaman mara lafiya da masu jinya cikin walwala, ta ce wannan abun a yaba wa gwamna ne da sauran mataimakansa a wannan lokaci.
A ƙarshe, ta ce dangane da walwala da jin daɗin ma’aikata kuwa, ta ce Gwamnan Kano, Alhaji Abba ya ɗauki matakin kula da jin daɗin da walwalan ma’aikatan asibitocin jihar baki ɗaya. Ta yaba wa ma’aikatan asibitin Sheikh Muhammad Jidda kan ƙoƙarinsu da jajircewarsu da haɗin kai da suke bayarwa kula da marasa lafiya kamar yadda doka ta tanada, wanda wannan shi ne babban abun farin ciki da aka samu ta kowana fanin a wannan asibiti.














