Gwamnatin Tarayya ta faɗaɗa shirin masu gadin dazuka zuwa jihohi 10, inda aka horas da sama da jami’ai 9,000 domin taimakawa wajen tsaron dazuka da sauran wuraren da masu garkuwa da mutane, ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka ke amfani da su a matsayin mafaka.
Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (ONSA) ne ke jagorantar shirin, yayin da Hukumar DSS ke kula da aiwatar da shi tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohi. Ana mayar da hankali ne kan dazuka, yankunan kan iyaka da wuraren da jami’an tsaro ke fuskantar matsalar isa gare su.
A sabon matakin shirin, an horas da sama da masu gadin dazuka 2,000 a Kaduna, Edo da Kogi, kuma ana shirin tura su wuraren da matsalar tsaro ta fi tsanani. Wannan ya biyo bayan horar da sama da 7,000 a Borno, Sokoto, Yobe, Adamawa, Neja, Kwara da Kebbi.
Gwamnati ta ce an tantance masu gadin dazukan tare da binciken tarihinsu kafin ɗaukar su aiki, sannan aka ba su horo kan sarrafa makamai, da sintiri, da tattara bayanan sirri, da gano hanyoyi da kare dazuka. Shirin na da nufin hana masu aikata laifuka amfani da dazuka wajen zirga-zirga, da kafa sansanoni ko ɓoye mutanen da suka yi garkuwa da su.
Gwamnonin Kaduna, da Edo da Kogi sun yaba wa ONSA kan jagorantar shirin, inda suka ce faɗaɗa masu gadin dazuka zai ƙarfafa tsaro tare da taimaka wa gwamnati wajen isa ga yankunan da jami’an tsaro ba sa iya kaiwa yadda ya kamata.














