Wata ƙungiya a ƙarƙashin jam’iyyar APC a Jihar Bauchi ta bayyana cewa ba za ta marabci gwamnan jihar, Bala Mohammed, ba idan ya sauya sheƙa daga PDP.
Ƙungiyar, wadda ke aiki da sunan APC Solidarity Group & Allied Associations, ta bayyana matsayarta ne a wata sanarwa da jami’anta I.B. Muhammad da Abubakar Abdullahi suka sanya wa hannu, inda suka ce sun aika takarda ga shugaban APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, suna bayyana dalilai 10 da suka sa ba su goyon bayan shigar gwamnan cikin jam’iyyar.
- Gwamnatin Bauchi Ta Rufe Kasuwannin Shanu 25 Saboda Matsalar Tsaro
- Asusun IMF Ya Bude Cibiyarsa Ta Shiyyar Asiya Da Pasifik A Shanghai
A cewar ƙungiyar, suna da damuwa kan yadda gwamnan ke yawan sukar jam’iyyar APC da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, abin da suka ce na kawo cikas ga martabar jam’iyyar. Sun kuma yi nuni da rikice-rikicen siyasa tsakaninsa da manyan jiga-jigan APC a jihar.
Ƙungiyar ta gargadi cewa karɓar gwamnan na iya haifar da saɓani a cikin jam’iyyar tare da raunana damar APC a zaɓen 2027, tana mai cewa hakan zai iya karya gwuiwar tsofaffin mambobin da suka daɗe suna biyayya ga jam’iyyar.
Ta ƙara da cewa APC ta fi kowa girma, don haka dole ne shugabanni su mayar da hankali kan haɗin kai da tsare-tsare domin samun nasara a zaɓukan gaba, tare da kira ga dukkan mambobi su haɗa kai wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar a Bauchi da ƙasa baki ɗaya.















Discussion about this post