Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bai wa iyalan marigayi Laftanar Kanal OC Okolo gudunmawar Naira miliyan 50, wanda aka kashe a harin Boko Haram a Mandaragirau, Ƙaramar Hukumar Biu.
A wata sanarwa da mai ba gwamnan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Dauda Iliya, ya fitar, an ce gudunmawar na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na tallafawa iyalan jami’an tsaro da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa.
- A Tattauna Da Boko Haram Don Sako Mana Mutane 416 Da Aka Kama – Ƙungiya A Borno
- Gwamna AbdulRazaq Ya Tallafa Wa Iyalan Sojojin Da Aka Kashe Da ₦60m
An bayyana cewa gwamnan, wanda wakilinsa mai ba shi shawara kan tsaro, Birgediya Janar Abdullahi Sabi Ishaq mai ritaya, ya gabatar da tallafin yayin jana’izar marigayin da aka gudanar a Obinofia Ndiuno da ke Jihar Enugu.
Gwamnan ya kuma jaddada cewa zai ci gaba da kai ziyara ga iyalan sauran jami’an da suka mutu ko suka ɓace a yayin aiki, yana mai cewa gudunmawar na nuna goyon bayan gwamnatin Borno ga jaruman da suka mutu da kuma waɗanda suka jikkata a yaƙi da ta’addanci.
A nasa ɓangaren, wakilin iyalan marigayin, Farfesa Stanley Okolo, ya gode wa gwamnan bisa wannan karamci, yana mai cewa iyalan sun ji daɗin tallafin da kuma tawagar da aka tura daga Maiduguri domin halartar jana’izar duk da gajeren lokaci na sanarwa.















Discussion about this post