ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Rundunar Ƴansandan Nijeriya ta tabbatar da kisan jami’anta 17 da kuma wasu sojoji da ba a bayyana adadinsu ba a wani hari da ƴan ta’addan Boko Haram suka kai Makarantar Horar da Runduna ta Musamman ta Sojojin Nijeriya da ke Buni Yadi, a Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe.

Kakakin rundunar ƴansandan, Anthony Okon Placid, ne ya tabbatar da harin a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, 16 ga Mayun 2026.

Placid ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:15 na dare a ranar 8 ga Mayun 2026.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa jami’an ƴansandan suna cikin horarwar dabarun yaƙi da ta’addanci lokacin da ƴan bindigar suka kai wani harin haɗin gwiwa daga wurare daban-daban kan sansanin sojin.

“Jami’an sun sadaukar da rayukansu wajen bautawa ƙasa bayan harin ta’addanci da aka kai Makarantar Horar da Runduna ta Musamman ta Sojojin Nijeriya da ke Buni Yadi,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Ya ƙara da cewa wasu sojoji ma sun mutu yayin da suke ƙoƙarin daƙile harin, sai dai bai bayyana adadin sojojin da suka mutu ba. Rundunar sojin Nijeriya ma ba ta fitar da cikakken adadin ba.

Majiyoyi a Buni Yadi sun ce maharan sun yi artabu mai tsanani da jami’an tsaro wanda ya ɗauki sama da sa’o’i uku.

“‘Yan ta’addan sun janye da misalin ƙarfe 4:00 na safe bayan sun kashe jami’an ƴansanda 17 da sama da sojoji 20,” in ji wani ɗan ƙungiyar Sa Kai.

Ya ƙara da cewa sojoji sun kwashe gawarwakin jami’ansu nan take bayan artabun, yayin da ƴansanda ba su samu damar kwashe gawarwakin jami’ansu ba sai washegari.

“Daga baya ƴansanda sun kwashe gawarwakin zuwa ɗakin ajiye gawa na Asibitin Koyarwa na Jami’a da ke Damaturu, daga inda motocin ƴansanda suka kai su Maiduguri,” in ji shi.

Ya bayyana lamarin a matsayin ɗaya daga cikin mafi munin artabu da aka gani a baya-bayan nan, yana mai cewa jami’an tsaro da mazauna yankin sun yarda cewa ba su taɓa ganin irin wannan ba tun bayan fara tayar da ƙayar bayan Boko Haram.

“Musayar wutar da muka gani a wannan dare ta bambanta. Ba mu taɓa ganin irinta ba tun bayan fara rikicin Boko Haram,” in ji shi.

Ya kuma ce daga ƙarshe ƴan ta’addan sun ja da baya bayan sun fahimci cewa ba za su iya ƙwace sansanin ba, ko sace makamai da lalata kayan aikin soja.

A baya ma ƴan Boko Haram sun sha ƙoƙarin ƙwace sansanonin soja a yankin saboda muhimmancin Buni Yadi wajen ayyukan yaƙi da ta’addanci a Arewa maso Gabas.

Sufeto Janar na Ƴansanda, Olatunji Disu, ya bayyana jami’an da suka mutu a matsayin jarumai masu kishin ƙasa da jajircewa wajen kare tsaron ƙasa.

Ya tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa rundunar ƴansanda tare da haɗin gwiwar rundunar soji da sauran hukumomin tsaro za su ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka kai harin domin hukunta su.

A wani ɓangaren kuma, Kwamishinan Ƴansandan Jihar Yobe, Usman Jibrin, ya kai ziyara Makarantar Horar da Runduna ta Musamman ta Sojojin Nijeriya a madadin Sufeto Janar, inda ya gana da kwamandan makarantar, Birgediya Janar A.C. Enuagu, sauran jami’an soja da kuma ƴansandan da suka tsira daga horarwar.

Ya ƙarfafa wa sauran waɗanda ke samun horarwa gwiwa da su ci gaba da kammala shirin horarwar domin girmama abokan aikinsu da suka rasu.

Ya sake jaddada cewa rundunar ƴansanda tare da haɗin gwiwar rundunar soji da sauran hukumomin tsaro za su ci gaba da aiki domin tabbatar da kama maharan tare da hukunta su.

Mazauna garin Buni Yadi sun nuna alhini matuƙa kan kashe jami’an ƴansanda da sojojin.

Wani mazaunin yankin, wanda ya ce ya yi karatu tare da ɗaya daga cikin jami’an da aka kashe, ya bayyana cewa al’umma sun yi ƙoƙarin neman a ba su gawarwakin domin gudanar da jana’iza.

“Abin takaici, an ƙi amincewa da buƙatarmu a Asibitin Koyarwa na Jami’a da ke Damaturu kafin a kai gawarwakin Maiduguri inda aka yi musu jana’iza,” in ji shi.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Kotu Ta Ba Da Belin El-Rufai Kan Naira Miliyan 100

Kotu Ta Ba Da Belin El-Rufai Kan Naira Miliyan 100

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.