Rundunar Ƴansandan Nijeriya ta tabbatar da kisan jami’anta 17 da kuma wasu sojoji da ba a bayyana adadinsu ba a wani hari da ƴan ta’addan Boko Haram suka kai Makarantar Horar da Runduna ta Musamman ta Sojojin Nijeriya da ke Buni Yadi, a Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe.
Kakakin rundunar ƴansandan, Anthony Okon Placid, ne ya tabbatar da harin a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, 16 ga Mayun 2026.
Placid ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:15 na dare a ranar 8 ga Mayun 2026.
Ya bayyana cewa jami’an ƴansandan suna cikin horarwar dabarun yaƙi da ta’addanci lokacin da ƴan bindigar suka kai wani harin haɗin gwiwa daga wurare daban-daban kan sansanin sojin.
“Jami’an sun sadaukar da rayukansu wajen bautawa ƙasa bayan harin ta’addanci da aka kai Makarantar Horar da Runduna ta Musamman ta Sojojin Nijeriya da ke Buni Yadi,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa wasu sojoji ma sun mutu yayin da suke ƙoƙarin daƙile harin, sai dai bai bayyana adadin sojojin da suka mutu ba. Rundunar sojin Nijeriya ma ba ta fitar da cikakken adadin ba.
Majiyoyi a Buni Yadi sun ce maharan sun yi artabu mai tsanani da jami’an tsaro wanda ya ɗauki sama da sa’o’i uku.
“‘Yan ta’addan sun janye da misalin ƙarfe 4:00 na safe bayan sun kashe jami’an ƴansanda 17 da sama da sojoji 20,” in ji wani ɗan ƙungiyar Sa Kai.
Ya ƙara da cewa sojoji sun kwashe gawarwakin jami’ansu nan take bayan artabun, yayin da ƴansanda ba su samu damar kwashe gawarwakin jami’ansu ba sai washegari.
“Daga baya ƴansanda sun kwashe gawarwakin zuwa ɗakin ajiye gawa na Asibitin Koyarwa na Jami’a da ke Damaturu, daga inda motocin ƴansanda suka kai su Maiduguri,” in ji shi.
Ya bayyana lamarin a matsayin ɗaya daga cikin mafi munin artabu da aka gani a baya-bayan nan, yana mai cewa jami’an tsaro da mazauna yankin sun yarda cewa ba su taɓa ganin irin wannan ba tun bayan fara tayar da ƙayar bayan Boko Haram.
“Musayar wutar da muka gani a wannan dare ta bambanta. Ba mu taɓa ganin irinta ba tun bayan fara rikicin Boko Haram,” in ji shi.
Ya kuma ce daga ƙarshe ƴan ta’addan sun ja da baya bayan sun fahimci cewa ba za su iya ƙwace sansanin ba, ko sace makamai da lalata kayan aikin soja.
A baya ma ƴan Boko Haram sun sha ƙoƙarin ƙwace sansanonin soja a yankin saboda muhimmancin Buni Yadi wajen ayyukan yaƙi da ta’addanci a Arewa maso Gabas.
Sufeto Janar na Ƴansanda, Olatunji Disu, ya bayyana jami’an da suka mutu a matsayin jarumai masu kishin ƙasa da jajircewa wajen kare tsaron ƙasa.
Ya tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa rundunar ƴansanda tare da haɗin gwiwar rundunar soji da sauran hukumomin tsaro za su ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka kai harin domin hukunta su.
A wani ɓangaren kuma, Kwamishinan Ƴansandan Jihar Yobe, Usman Jibrin, ya kai ziyara Makarantar Horar da Runduna ta Musamman ta Sojojin Nijeriya a madadin Sufeto Janar, inda ya gana da kwamandan makarantar, Birgediya Janar A.C. Enuagu, sauran jami’an soja da kuma ƴansandan da suka tsira daga horarwar.
Ya ƙarfafa wa sauran waɗanda ke samun horarwa gwiwa da su ci gaba da kammala shirin horarwar domin girmama abokan aikinsu da suka rasu.
Ya sake jaddada cewa rundunar ƴansanda tare da haɗin gwiwar rundunar soji da sauran hukumomin tsaro za su ci gaba da aiki domin tabbatar da kama maharan tare da hukunta su.
Mazauna garin Buni Yadi sun nuna alhini matuƙa kan kashe jami’an ƴansanda da sojojin.
Wani mazaunin yankin, wanda ya ce ya yi karatu tare da ɗaya daga cikin jami’an da aka kashe, ya bayyana cewa al’umma sun yi ƙoƙarin neman a ba su gawarwakin domin gudanar da jana’iza.
“Abin takaici, an ƙi amincewa da buƙatarmu a Asibitin Koyarwa na Jami’a da ke Damaturu kafin a kai gawarwakin Maiduguri inda aka yi musu jana’iza,” in ji shi.















Discussion about this post