ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

by Rabi'u Ali Indabawa
4 hours ago
'Yansanda

Rundunar ’Yansandan Jihar Borno ta yi nasarar ceto wani yaro mai shekaru shida da aka yi garkuwa da shi a Maiduguri, tare da kama wani mutum da ake zargi da hannu a aikata laifin.

Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da kakakinta, Nahum Daso, ya fitar a ranar Litinin.

A cewar Daso, yaron mai suna Alkali Musa, mazaunin unguwar Mafoni da ke Maiduguri, ya bace ne bayan ya fita wasa a ranar 6 ga Yuni amma bai dawo gida ba.

ADVERTISEMENT

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce binciken farko ya nuna cewa jim kadan bayan batan yaron, wanda ake zargin ya tuntubi iyayensa tare da neman kudin fansa na Naira 200,000 kafin a sake shi.

Ya bayyana cewa bayan samun rahoton lamarin a ranar Lahadi, DPO na ofishin ’yansanda na Lamisula ya tattara tawagar jami’an bincike tare da kaddamar da wani aiki na musamman na tattara bayanan sirri domin gano wanda ake zargin da kuma ceto yaron.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

Sanarwar ta ce: “A ranar 7 ga Yuni, 2026, da misalin karfe 2:00 na rana, rundunar ta samu rahoton batan wani yaro mai suna Alkali Musa, dan shekara shida daga yankin Mafoni a Maiduguri, wanda ya fita wasa a ranar 6 ga Yuni, 2026 amma bai dawo gida ba.

“Binciken farko ya nuna cewa jim kadan bayan batan yaron, wanda ake zargin ya tuntubi iyayensa tare da neman kudin fansa har Naira 200,000 domin a sake shi.”

Daso ya ce wannan aiki ya kai ga cafke wanda ake zargin, mai suna Ali Alhaji Ali, tare da ceto yaron cikin koshin lafiya.

Sanarwar ta kara da cewa an ceto yaron ba tare da ya ji rauni ba, sannan an hada shi da iyalansa.

“Kokarin da aka yi ya samar da sakamako mai kyau, inda aka kama wanda ake zargin, Ali Alhaji Ali, tare da ceto yaron ba tare da wani rauni ba.

“Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, kuma an mika shari’ar zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin ci gaba da bincike da kuma yiwuwar gurfanar da shi a kotu,” in ji sanarwar.

Da yake mayar da martani, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin bisa saurin martani da kwarewar da suka nuna.

Ya kuma tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

“Kwamishinan ’Yansanda na Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya yaba da saurin matakin da jami’an suka dauka a wannan aiki, tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

“Haka kuma rundunar tana kira ga iyaye da masu kula da yara da su kasance masu sa ido sosai kan ‘ya’yansu, tare da karfafa wa jama’a su rika kai rahoton duk wani mutum ko motsi da suke zargi ga ofishin ’yansanda mafi kusa,” in ji sanarwar.

A wani labari makamancin wannan, an ruwaito cewa a ranar 25 ga Afrilu, Rundunar ’Yansandan Jihar Kano ta ceto wani yaro dan shekara biyu da aka sace, tare da kama mutane uku da ake zargi da hannu a lamarin, sannan ta kwato Naira 930,000 daga cikin kudin fansar da iyalan yaron suka biya.

Kakakin rundunar a Kano, Abdullahi Kiyawa, ya bayyana cewa an yi garkuwa da yaron ne kafin daga bisani jami’an tsaro su ceto shi ta hanyar wani aiki na musamman da ya dogara da bayanan sirri.

'Yansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

MASU ALAKA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

June 6, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.