ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
'Yansanda

Rundunar ’Yansandan Jihar Borno ta yi nasarar ceto wani yaro mai shekaru shida da aka yi garkuwa da shi a Maiduguri, tare da kama wani mutum da ake zargi da hannu a aikata laifin.

Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da kakakinta, Nahum Daso, ya fitar a ranar Litinin.

A cewar Daso, yaron mai suna Alkali Musa, mazaunin unguwar Mafoni da ke Maiduguri, ya bace ne bayan ya fita wasa a ranar 6 ga Yuni amma bai dawo gida ba.

ADVERTISEMENT

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce binciken farko ya nuna cewa jim kadan bayan batan yaron, wanda ake zargin ya tuntubi iyayensa tare da neman kudin fansa na Naira 200,000 kafin a sake shi.

Ya bayyana cewa bayan samun rahoton lamarin a ranar Lahadi, DPO na ofishin ’yansanda na Lamisula ya tattara tawagar jami’an bincike tare da kaddamar da wani aiki na musamman na tattara bayanan sirri domin gano wanda ake zargin da kuma ceto yaron.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Sanarwar ta ce: “A ranar 7 ga Yuni, 2026, da misalin karfe 2:00 na rana, rundunar ta samu rahoton batan wani yaro mai suna Alkali Musa, dan shekara shida daga yankin Mafoni a Maiduguri, wanda ya fita wasa a ranar 6 ga Yuni, 2026 amma bai dawo gida ba.

“Binciken farko ya nuna cewa jim kadan bayan batan yaron, wanda ake zargin ya tuntubi iyayensa tare da neman kudin fansa har Naira 200,000 domin a sake shi.”

Daso ya ce wannan aiki ya kai ga cafke wanda ake zargin, mai suna Ali Alhaji Ali, tare da ceto yaron cikin koshin lafiya.

Sanarwar ta kara da cewa an ceto yaron ba tare da ya ji rauni ba, sannan an hada shi da iyalansa.

“Kokarin da aka yi ya samar da sakamako mai kyau, inda aka kama wanda ake zargin, Ali Alhaji Ali, tare da ceto yaron ba tare da wani rauni ba.

“Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, kuma an mika shari’ar zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin ci gaba da bincike da kuma yiwuwar gurfanar da shi a kotu,” in ji sanarwar.

Da yake mayar da martani, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin bisa saurin martani da kwarewar da suka nuna.

Ya kuma tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

“Kwamishinan ’Yansanda na Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya yaba da saurin matakin da jami’an suka dauka a wannan aiki, tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

“Haka kuma rundunar tana kira ga iyaye da masu kula da yara da su kasance masu sa ido sosai kan ‘ya’yansu, tare da karfafa wa jama’a su rika kai rahoton duk wani mutum ko motsi da suke zargi ga ofishin ’yansanda mafi kusa,” in ji sanarwar.

A wani labari makamancin wannan, an ruwaito cewa a ranar 25 ga Afrilu, Rundunar ’Yansandan Jihar Kano ta ceto wani yaro dan shekara biyu da aka sace, tare da kama mutane uku da ake zargi da hannu a lamarin, sannan ta kwato Naira 930,000 daga cikin kudin fansar da iyalan yaron suka biya.

Kakakin rundunar a Kano, Abdullahi Kiyawa, ya bayyana cewa an yi garkuwa da yaron ne kafin daga bisani jami’an tsaro su ceto shi ta hanyar wani aiki na musamman da ya dogara da bayanan sirri.

'Yansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

LABARAI MASU NASABA

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.