Rundunar ’Yansandan Jihar Borno ta yi nasarar ceto wani yaro mai shekaru shida da aka yi garkuwa da shi a Maiduguri, tare da kama wani mutum da ake zargi da hannu a aikata laifin.
Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da kakakinta, Nahum Daso, ya fitar a ranar Litinin.
A cewar Daso, yaron mai suna Alkali Musa, mazaunin unguwar Mafoni da ke Maiduguri, ya bace ne bayan ya fita wasa a ranar 6 ga Yuni amma bai dawo gida ba.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce binciken farko ya nuna cewa jim kadan bayan batan yaron, wanda ake zargin ya tuntubi iyayensa tare da neman kudin fansa na Naira 200,000 kafin a sake shi.
Ya bayyana cewa bayan samun rahoton lamarin a ranar Lahadi, DPO na ofishin ’yansanda na Lamisula ya tattara tawagar jami’an bincike tare da kaddamar da wani aiki na musamman na tattara bayanan sirri domin gano wanda ake zargin da kuma ceto yaron.
Sanarwar ta ce: “A ranar 7 ga Yuni, 2026, da misalin karfe 2:00 na rana, rundunar ta samu rahoton batan wani yaro mai suna Alkali Musa, dan shekara shida daga yankin Mafoni a Maiduguri, wanda ya fita wasa a ranar 6 ga Yuni, 2026 amma bai dawo gida ba.
“Binciken farko ya nuna cewa jim kadan bayan batan yaron, wanda ake zargin ya tuntubi iyayensa tare da neman kudin fansa har Naira 200,000 domin a sake shi.”
Daso ya ce wannan aiki ya kai ga cafke wanda ake zargin, mai suna Ali Alhaji Ali, tare da ceto yaron cikin koshin lafiya.
Sanarwar ta kara da cewa an ceto yaron ba tare da ya ji rauni ba, sannan an hada shi da iyalansa.
“Kokarin da aka yi ya samar da sakamako mai kyau, inda aka kama wanda ake zargin, Ali Alhaji Ali, tare da ceto yaron ba tare da wani rauni ba.
“Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, kuma an mika shari’ar zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin ci gaba da bincike da kuma yiwuwar gurfanar da shi a kotu,” in ji sanarwar.
Da yake mayar da martani, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin bisa saurin martani da kwarewar da suka nuna.
Ya kuma tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
“Kwamishinan ’Yansanda na Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya yaba da saurin matakin da jami’an suka dauka a wannan aiki, tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.
“Haka kuma rundunar tana kira ga iyaye da masu kula da yara da su kasance masu sa ido sosai kan ‘ya’yansu, tare da karfafa wa jama’a su rika kai rahoton duk wani mutum ko motsi da suke zargi ga ofishin ’yansanda mafi kusa,” in ji sanarwar.
A wani labari makamancin wannan, an ruwaito cewa a ranar 25 ga Afrilu, Rundunar ’Yansandan Jihar Kano ta ceto wani yaro dan shekara biyu da aka sace, tare da kama mutane uku da ake zargi da hannu a lamarin, sannan ta kwato Naira 930,000 daga cikin kudin fansar da iyalan yaron suka biya.
Kakakin rundunar a Kano, Abdullahi Kiyawa, ya bayyana cewa an yi garkuwa da yaron ne kafin daga bisani jami’an tsaro su ceto shi ta hanyar wani aiki na musamman da ya dogara da bayanan sirri.















Discussion about this post