ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
DANGOTE

Kamfanin Sufurin Siminti na Dangote, ya kara fadada shirye-shirye masu tasiri tare da amfani da fasahohin zamani domin inganta aiki, shugabanci nagari da kuma bin ka’idojin tsaron hanya.

A wata sanarwa da Sashen Hulda da Jama’a da Sadarwar kamfanin ya fitar, an bayyana cewa sabbin shirye-shiryen sun shafi muhimman fannoni na gudanar da ayyuka, ciki har da auna kwazon aiki, karfafa ka’idojin shugabanci da inganta tsarin daukar alhaki.

Sanarwar ta kara da cewa shirye-shiryen sun kuma hada da horar da direbobi tare da bunkasa kwarewarsu, amfani da tsarin tsaro na zamani da ke aiki da fasaha, tsara zirga-zirga cikin tsari, da kuma sabunta takardun cancanta akai-akai.

ADVERTISEMENT

Sauran shirye-shiryen sun hada da gwajin miyagun kwayoyi ga direbobi, kulla hadin gwiwa da sauran hukumomi da kungiyoyi, aiwatar da manufofin muhalli, zamantakewa da shugabanci (ESG), shirye-shiryen dorewar ci gaba da kuma ayyukan tallafa wa al’umma.

Sanarwar da kakakin kamfanin, Anthony Chiejina, ya sanya wa hannu ta tunatar da cewa Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta yaba wa kamfanin kan shirye-shiryensa na tsaron hanya, wadanda suka taimaka wajen rage haduran mota a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

An kuma ambato Shugaban Sashen Sufuri na kamfanin, Murilo Silba, yana cewa kamfanin ya inganta tsarin gudanar da harkokin sufuri ta hanyar amfani da na’urorin bincike masu sarrafa kansu da kuma hanyoyin da ke amfani da basirar wucin gadi (AI) domin kara ingancin aiki da tsaron hanya.

Silba ya bayyana cewa kamfanin ya kuma girke ingantattun na’urorin GPS da tsarin telematics domin sa ido kan halayen direbobi a lokacin tafiya kai tsaye, lamarin da ke kara karfafawa kulawa da kuma tabbatar da tsaro a dukkan motocin kamfanin.

Ya kara da cewa, a kokarin da kamfanin ke yi na rage gajiyar direbobi, ya kara fadada shirye-shiryen kula da lafiyarsu tare da gudanar da tarurruka daban-daban da masu motocin dakon kaya da direbobinsu domin karfafa wayar da kai kan tsaro, bin ka’idoji da daukar alhaki a kan hanya.

Mista Murilo Silba ya ce hadin gwiwar da kamfanin ke yi da Hukumar Kiyaye Hadura (FRSC) ya fara samar da sakamako mai kyau, yana mai cewa wannan hadin gwiwa na ci gaba da karfafa ka’idojin tsaro a dukkan ayyukan kamfanin.

Ya kara da cewa jami’an FRSC na taka muhimmiyar rawa wajen horaswa da tantance direbobi a Makarantar Koyar da Tukin Motocin Dakon Kaya ta Dangote da ke Obajana, inda suke ba da shawarwari na fasaha, tabbatar da bin ka’idojin aiki mafi inganci da kuma taimakawa wajen samar da kwararrun direbobi masu kishin tsaro.

A cewarsa, adadin direbobin da ke samun horo cikin tsari, gwajin miyagun kwayoyi da barasa, da kuma sabunta takardun cancanta lokaci-lokaci ya karu sosai, inda ya bayyana wannan ci gaban a matsayin “mai ban mamaki kwarai.”

Silba ya bayyana cewa tsakanin zangon farko na shekarun 2025 da 2026, kamfanin Dangote Simintin na Obajana ya samu gagarumin ci gaba wajen bin matakan tsaro. Gwajin miyagun kwayoyi da barasa ya karu da kashi 245.2 cikin dari, binciken motocin kafin fara tafiya ya karu da kashi 489.1 cikin dari, yayin da shirye-shiryen horar da direbobi suka karu da kashi 128.4 cikin dari.

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar FRSC, Shehu Mohammed, ya yaba wa kamfanin kan kafa sabbin ma’aunai wajen gudanar da tsaron hanya, tare da karfafa shi da ya ci gaba da aiwatar da gyare-gyaren da suka taimaka wajen inganta tsaro a fannin sufuri a Nijeriya.

Corps Marshal din ya bayyana cewa idan aka kwatanta shekarun 2025 da 2026, haduran da suka shafi manyan motocin kamfanin Dangote Cement sun ragu da kashi 56 cikin dari, mace-macen da suka biyo bayan irin wadannan hadurran sun ragu da kashi 36 cikin dari, yayin da yawan raunuka ya ragu da kashi 52 cikin dari.

Ya ce wannan ci gaban ya nuna cewa kamfanin ya aiwatar da shirin nazarin gibin da ke akwai da kuma manufofin gudanarwa da ya kamata sauran kamfanonin sufuri da dabaru a Afirka su yi koyi da su.

Ya ce: “Mun dade muna cewa idan Kamfanin Simintin Dangote ya yi abin da ya dace, Nijeriya da ma Afirka za su yi abin da ya dace. Wannan babban abin alfahari ne ga Nijeriya.”

DANGOTE
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

MASU ALAKA

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.