ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
DANGOTE

Kamfanin Sufurin Siminti na Dangote, ya kara fadada shirye-shirye masu tasiri tare da amfani da fasahohin zamani domin inganta aiki, shugabanci nagari da kuma bin ka’idojin tsaron hanya.

A wata sanarwa da Sashen Hulda da Jama’a da Sadarwar kamfanin ya fitar, an bayyana cewa sabbin shirye-shiryen sun shafi muhimman fannoni na gudanar da ayyuka, ciki har da auna kwazon aiki, karfafa ka’idojin shugabanci da inganta tsarin daukar alhaki.

Sanarwar ta kara da cewa shirye-shiryen sun kuma hada da horar da direbobi tare da bunkasa kwarewarsu, amfani da tsarin tsaro na zamani da ke aiki da fasaha, tsara zirga-zirga cikin tsari, da kuma sabunta takardun cancanta akai-akai.

ADVERTISEMENT

Sauran shirye-shiryen sun hada da gwajin miyagun kwayoyi ga direbobi, kulla hadin gwiwa da sauran hukumomi da kungiyoyi, aiwatar da manufofin muhalli, zamantakewa da shugabanci (ESG), shirye-shiryen dorewar ci gaba da kuma ayyukan tallafa wa al’umma.

Sanarwar da kakakin kamfanin, Anthony Chiejina, ya sanya wa hannu ta tunatar da cewa Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta yaba wa kamfanin kan shirye-shiryensa na tsaron hanya, wadanda suka taimaka wajen rage haduran mota a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

An kuma ambato Shugaban Sashen Sufuri na kamfanin, Murilo Silba, yana cewa kamfanin ya inganta tsarin gudanar da harkokin sufuri ta hanyar amfani da na’urorin bincike masu sarrafa kansu da kuma hanyoyin da ke amfani da basirar wucin gadi (AI) domin kara ingancin aiki da tsaron hanya.

Silba ya bayyana cewa kamfanin ya kuma girke ingantattun na’urorin GPS da tsarin telematics domin sa ido kan halayen direbobi a lokacin tafiya kai tsaye, lamarin da ke kara karfafawa kulawa da kuma tabbatar da tsaro a dukkan motocin kamfanin.

Ya kara da cewa, a kokarin da kamfanin ke yi na rage gajiyar direbobi, ya kara fadada shirye-shiryen kula da lafiyarsu tare da gudanar da tarurruka daban-daban da masu motocin dakon kaya da direbobinsu domin karfafa wayar da kai kan tsaro, bin ka’idoji da daukar alhaki a kan hanya.

Mista Murilo Silba ya ce hadin gwiwar da kamfanin ke yi da Hukumar Kiyaye Hadura (FRSC) ya fara samar da sakamako mai kyau, yana mai cewa wannan hadin gwiwa na ci gaba da karfafa ka’idojin tsaro a dukkan ayyukan kamfanin.

Ya kara da cewa jami’an FRSC na taka muhimmiyar rawa wajen horaswa da tantance direbobi a Makarantar Koyar da Tukin Motocin Dakon Kaya ta Dangote da ke Obajana, inda suke ba da shawarwari na fasaha, tabbatar da bin ka’idojin aiki mafi inganci da kuma taimakawa wajen samar da kwararrun direbobi masu kishin tsaro.

A cewarsa, adadin direbobin da ke samun horo cikin tsari, gwajin miyagun kwayoyi da barasa, da kuma sabunta takardun cancanta lokaci-lokaci ya karu sosai, inda ya bayyana wannan ci gaban a matsayin “mai ban mamaki kwarai.”

Silba ya bayyana cewa tsakanin zangon farko na shekarun 2025 da 2026, kamfanin Dangote Simintin na Obajana ya samu gagarumin ci gaba wajen bin matakan tsaro. Gwajin miyagun kwayoyi da barasa ya karu da kashi 245.2 cikin dari, binciken motocin kafin fara tafiya ya karu da kashi 489.1 cikin dari, yayin da shirye-shiryen horar da direbobi suka karu da kashi 128.4 cikin dari.

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar FRSC, Shehu Mohammed, ya yaba wa kamfanin kan kafa sabbin ma’aunai wajen gudanar da tsaron hanya, tare da karfafa shi da ya ci gaba da aiwatar da gyare-gyaren da suka taimaka wajen inganta tsaro a fannin sufuri a Nijeriya.

Corps Marshal din ya bayyana cewa idan aka kwatanta shekarun 2025 da 2026, haduran da suka shafi manyan motocin kamfanin Dangote Cement sun ragu da kashi 56 cikin dari, mace-macen da suka biyo bayan irin wadannan hadurran sun ragu da kashi 36 cikin dari, yayin da yawan raunuka ya ragu da kashi 52 cikin dari.

Ya ce wannan ci gaban ya nuna cewa kamfanin ya aiwatar da shirin nazarin gibin da ke akwai da kuma manufofin gudanarwa da ya kamata sauran kamfanonin sufuri da dabaru a Afirka su yi koyi da su.

Ya ce: “Mun dade muna cewa idan Kamfanin Simintin Dangote ya yi abin da ya dace, Nijeriya da ma Afirka za su yi abin da ya dace. Wannan babban abin alfahari ne ga Nijeriya.”

DANGOTE
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.