Rundunar ’Yansandan Jihar Adamawa ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da aikata laifin fashi da makami a Karamar Hukumar Yola ta Arewa.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Suleiman Nguroje, ya fitar a ranar Talata, ya ce jami’an ’yansanda da ke aiki a Hedikwatar ’Yansanda ta Doubeli ne suka kama mutanen biyu dangane da wasu laifuka daban-daban.
“Ranar 3 ga Yuni, 2026, jami’an ’yansanda sun kama wani Idris Auwal mai shekaru 22, mazaunin Doubeli Culbert da ke Karamar Hukumar Yola ta Arewa,” in ji sanarwar.
Binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ya hada baki da wasu mutum uku da har yanzu suka tsere, inda suka kutsa cikin wani shago da ke Nassarawo Borehole mallakin Abdullahi Sunusi.
Sanarwar ta ce wadanda ake zargin sun sace jaka mai dauke da kudi, muhimman takardu da kayayyakin masarufi na shago da darajarsu ba a bayyana ba.
“Bayan gudanar da bincike mai zurfi, an samu nasarar kama Idris Auwal, yayin da ake ci gaba da kokarin cafke sauran abokan aikinsa da suka tsere.”
A wani makamancin lamari da ya faru a ranar 5 ga Yuni, 2026, jami’an rundunar da ke Doubeli sun kama wani da ake zargin dan kungiyar ‘Shilla’ ne, wadda ta shahara wajen kai hare-hare da kwace kayan jama’a.
Sanarwar ta ce wanda ake zargin ya tare wani Abubakar Abdullahi a hanyar Doubeli Bypass dauke da adda, inda ya kwace masa wayar salula kirar Itel da kuma kudi Naira 19,000.
An kuma bayyana cewa wanda ake zargin ya ji wa wanda abin ya shafa rauni a kai da adda.
“Abin farin ciki, jami’an ’yansanda sun isa wurin cikin gaggawa, suka kama wanda ake zargin tare da tabbatar da cewa an kai wanda aka kai wa harin asibiti domin samun kulawar gaggawa.”
Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da adda, wuka da kuma wayar salular da aka sace.
Nguroje ya ce ana ci gaba da bincike kan mutanen biyu, yayin da rundunar ke kara kaimi wajen cafke sauran ’yan kungiyar da suka tsere domin gurfanar da su a gaban shari’a.
Rundunar ta tabbatar wa jama’a da jajircewarta wajen yaki da ayyukan kungiyar Shilla da sauran nau’o’in laifuffuka.
Ya kuma bukaci mazauna jihar da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai cikin lokaci domin inganta tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.














Discussion about this post