ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
Adamawa

Rundunar ’Yansandan Jihar Adamawa ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da aikata laifin fashi da makami a Karamar Hukumar Yola ta Arewa.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Suleiman Nguroje, ya fitar a ranar Talata, ya ce jami’an ’yansanda da ke aiki a Hedikwatar ’Yansanda ta Doubeli ne suka kama mutanen biyu dangane da wasu laifuka daban-daban.

“Ranar 3 ga Yuni, 2026, jami’an ’yansanda sun kama wani Idris Auwal mai shekaru 22, mazaunin Doubeli Culbert da ke Karamar Hukumar Yola ta Arewa,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT

Binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ya hada baki da wasu mutum uku da har yanzu suka tsere, inda suka kutsa cikin wani shago da ke Nassarawo Borehole mallakin Abdullahi Sunusi.

Sanarwar ta ce wadanda ake zargin sun sace jaka mai dauke da kudi, muhimman takardu da kayayyakin masarufi na shago da darajarsu ba a bayyana ba.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

“Bayan gudanar da bincike mai zurfi, an samu nasarar kama Idris Auwal, yayin da ake ci gaba da kokarin cafke sauran abokan aikinsa da suka tsere.”

A wani makamancin lamari da ya faru a ranar 5 ga Yuni, 2026, jami’an rundunar da ke Doubeli sun kama wani da ake zargin dan kungiyar ‘Shilla’ ne, wadda ta shahara wajen kai hare-hare da kwace kayan jama’a.

Sanarwar ta ce wanda ake zargin ya tare wani Abubakar Abdullahi a hanyar Doubeli Bypass dauke da adda, inda ya kwace masa wayar salula kirar Itel da kuma kudi Naira 19,000.

An kuma bayyana cewa wanda ake zargin ya ji wa wanda abin ya shafa rauni a kai da adda.

“Abin farin ciki, jami’an ’yansanda sun isa wurin cikin gaggawa, suka kama wanda ake zargin tare da tabbatar da cewa an kai wanda aka kai wa harin asibiti domin samun kulawar gaggawa.”

Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da adda, wuka da kuma wayar salular da aka sace.

Nguroje ya ce ana ci gaba da bincike kan mutanen biyu, yayin da rundunar ke kara kaimi wajen cafke sauran ’yan kungiyar da suka tsere domin gurfanar da su a gaban shari’a.

Rundunar ta tabbatar wa jama’a da jajircewarta wajen yaki da ayyukan kungiyar Shilla da sauran nau’o’in laifuffuka.

Ya kuma bukaci mazauna jihar da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai cikin lokaci domin inganta tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Adamawa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya - Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Adamawa

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Adamawa

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.