Gwamnatin Jihar Nasarawa ta rufe shahararriyar kasuwar tumatir da kayan gwari da ke Lafia, babban birnin jihar, saboda rashin tsaftar muhalli.
Kwamishiniyar Muhalli da Ma’adinai ta jihar, Hon. Magrete Itake Elayo ce, ta bayar da umarnin rufe kasuwar a ranar Asabar, 29 ga watan Agusta, 2026, yayin gudanar da aikin tsaftar muhalli na wannan watan.
Kwamishiniyar ta ce an rufe kasuwar ne domin tilasta wa ’yan kasuwar daina zuba tumatir da ganyayyaki kai-tsaye a ƙasa ba tare da amfani da shimfiɗa ba.
Ta kuma nuna damuwa kan yadda ’yan kasuwar suka mayar da wani ɓangare na kasuwar wurin zubar da shara, lamarin da ya haifar da rashin tsafta.
Ta umarci jami’an tsaro da su rufe kasuwar har zuwa ranar Litinin, inda za a duba halin da kasuwar take ciki kafin yanke shawarar matakin da za a ɗauka.
A wani mataki kuma, kwamishiniyar ta ce za a ci gaba da tsare masu tuƙa kekunan Napep 37 da aka kama suna zirga-zirga a tituna a lokacin aikin tsaftar muhalli.
Ta ce za a yi wa matasan wa’azi da wayar da kai kafin a sake su, tare da jaddada muhimmancin bin dokokin tsaftar muhalli.
Kwamishiniyar ta yaba wa ma’aikatan gwamnati, jami’an tsaro da masu ‘yan sa-kai da suka shiga aikin tsaftar muhalli, tare da gode musu bisa goyon bayan da suka bayar.














