ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda Ya Tallafawa Manoma Da Kayan Aikin Gona Na Miliyoyin Naira A Nasarawa

by Sulaiman and Zubairu M Lawal
4 weeks ago

Tsohon Sufeto Janar na ’Yansndan Nijeriya, Mohammed Adamu Abubakar (Walin Lafia), ya tallafa wa manoma a yankin Nasarawa ta Yamma da kayan aikin gona da kudinsu ya kai miliyoyin naira.

Da yake jawabi yayin rabon tallafin, Mohammed Adamu Abubakar ya shawarci manoman da suka amfana da su yi amfani da kayan aikin yadda ya kamata, tare da gujewa sayar da su.

Ya ce bai kamata a bai wa mutum kayan da zai amfana da su tsawon shekaru, sannan ya sayar da su domin biyan bukatun kwana ɗaya ko shekara ɗaya ba.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, an zakulo manoman da suka amfana daga sassa daban-daban na ƙananan hukumomin yankin domin su samu damar cin gajiyar tallafin.“Mun duba bukatar al’umma, musamman yadda za a samu abinci mai yawa a Jihar Nasarawa. Kuma dole ne a yi amfani da kayan aikin gona na zamani. Duk da cewa suna da tsada, idan muka taimaka muku da su, za ku samar da abinci mai yawa ga al’umma,” inji shi.

Ya ƙara da cewa babban abin da manomi ke bukata shi ne kayan aikin da zai taimaka masa wajen bunƙasa noma da ƙara yawan amfanin gona.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Kayan aikin da aka rabawa manomanTallafin ya ƙunshi ƙananan taraktocin hannu guda 200, buhunan takin zamani guda 2,500, magungunan gona guda 1,800, injinan ban ruwa guda 60, gorar feshi guda 100, kekunan ɗaukar kaya guda 100, wulbaro guda 100, da kuma fatanya da shebur.

Haka kuma, an ware tallafin kuɗi ga kowace daga cikin gundumomi 59, wanda jimillarsa ta kai miliyan Naira 59.

Tallafin ya shafi al’ummomin yankin Nasarawa ta Yamma, waɗanda suka haɗa da ƙananan hukumomin Karu, Keffi, Kokona, Nasarawa da Toto, daga gundumomi 59.

A nasa jawabin, Daraktan Yaƙin Neman Zaɓen Mohammed Adamu Abubakar a Jam’iyyar SDP, Alhaji Abdullahi Yammani, ya jaddada wa magoya bayansa cewa Mohammed Adamu Abubakar yana nan daram wajen shirin tsayawa takarar Gwamnan Jihar Nasarawa a ƙarƙashin Jam’iyyar SDP a zaɓen 2027.

Yammani ya buƙaci magoya bayan jam’iyyar da su ƙara himma wajen ganin an samu sauyin gwamnati a jihar.Ya ce al’ummar Jihar Nasarawa sun gaji da abin da ya kira “mulkin mallaka” na Jam’iyyar APC, yana mai cewa SDP za ta kawo sauyin gwamnati da zai taimaka wa al’ummar jihar.

Ya kuma yi kira ga al’umma da su fito kwai da kwarkwata domin kada kuri’unsu, tare da tabbatar da cewa an ƙirga ƙuri’un a gabansu kuma an bi tsarin kare ƙuri’a har zuwa inda ya dace.

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Zubairu M Lawal
+ posts Bio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    2027: Miyetti Allah Ta Yi Barazanar Ƙauracewa APC Kan Ci Gaba da Tsare Boɗejo
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tsaftar Muhalli: Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kasuwar Tumatir A Lafia
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Samar Da Abinci Mai Gina Jiki: Gwamna Sule Ya Duba Gonakin Shinkafa A Jangwa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnatin Nasarawa Ta Gargaɗi Masu Tayar Da Fitina Da Sunan Siyasa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin A Watanni 7 Na Bana Ba Siddabaru Ba Ne

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin A Watanni 7 Na Bana Ba Siddabaru Ba Ne

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.