Shugabannin ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore sun yi barazanar cewa za su yi kira ga al’ummar Fulani da su kaurace wa zaɓen Jam’iyyar APC a 2027, matuƙar Gwamnatin Tarayya ba ta saki shugaban ƙungiyar, Alhaji Bello Bodejo ba.
Shugabannin ƙungiyar sun bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da suka gudanar ranar Laraba a harabar ofishin Bodejo da ke Kasuwar Maliya, Ƙaramar Hukumar Karu a Jihar Nasarawa, inda suka nuna rashin amincewarsu da ci gaba da tsare shugaban nasu.
A cikin wata sanarwa da Shugaban ƙungiyar na Arewa ta Tsakiya, Alhaji Idris Gidado Bebeji, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta roƙi Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi, SAN, da shugabannin APC da hukumomin tsaro da abin ya shafa, da su tabbatar da warware lamarin cikin adalci da bin doka.
Ƙungiyar ta ce Bodejo fitaccen jagora ne da ke fafutukar kare muradun Fulani makiyaya, tare da bayar da gudunmawa wajen samar da zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.
A cewar ƙungiyar, DSS ta kama Bodejo a Jalingo, Jihar Taraba, a ranar da ya bayyana aniyarsa ta neman kujerar Sanata mai wakiltar Taraba ta Tsakiya. Daga bisani aka miƙa shi ga EFCC, inda ya shafe kusan watanni huɗu a tsare.
Sanarwar ta ce bayan cika wasu sharuddan da suka wajaba domin a sake shi daga hannun EFCC, an sake shi, amma daga bisani DSS ta sake kama shi a ranar 28 ga Agusta, 2026.
Shugabannin ƙungiyar sun ce ci gaba da tsare Bodejo ya jefa dubban zawarawa da marayu cikin ƙuncin rayuwa, musamman yaran da suka ce karatunsu ya tsaya saboda Bodejo ne ke taimaka wajen biyan bukatunsu na yau da kullum.
Da yake jawabi, ɗaya daga cikin shugabannin ƙungiyar, Sulaiman Abdullahi, ya ce idan Gwamnatin Tinubu ta ƙi sakin Bodejo, za su yi kira ga Fulani a faɗin Nijeriya da su ƙaurace wa zaɓen APC a 2027.
Ya yi iƙirarin cewa a zaɓen 2023, Bodejo ya taka rawa wajen haɗa kan al’ummar Fulani domin marawa APC baya, yana mai cewa yanzu ƙungiyar za ta iya karkatar da goyon bayan Fulani zuwa wata jam’iyya idan ba a sake shi ba.
Sai dai ƙungiyar ta buƙaci mambobinta da sauran Fulani makiyaya su ci gaba da kasancewa cikin nutsuwa, zaman lafiya da bin doka, yayin da take amfani da hanyoyin kundin tsarin mulki wajen neman a sake shugaban ƙungiyar.














