Gwamnan jihar Gombe State, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yabawa yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani na kai tsaye na jam’iyyar APC domin zaɓen ‘yan majalisar wakilai, yana mai cewa an gudanar da shi cikin lumana da gaskiya duk da koke-koken da wasu mambobin jam’iyyar suka yi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan ya kada ƙuri’arsa a mazaɓar Jekadafari da ke ƙaramar hukumar Gombe. Ya ce APC iyali ɗaya ce, yana mai kira ga dukkan mambobi su haɗa kai domin nasarar jam’iyyar a babban zaɓen 2027.
Shi ma wakilin shalƙwatar APC na ƙasa kuma shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani a jihar, Musa Kafur, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da zaɓen.
Jami’in gudanar da zaɓe a cibiyar Jekadafari, Yahaya Ibrahim Makeri, ya ayyana Saddam Bello a matsayin wanda ya lashe tikitin mazabar Gombe/Kwami/Funakaye bayan ya kayar da Zakariyya Jidda.
Sai dai duk da yabon da shugabannin jam’iyyar suka yi, wasu mambobin APC sun nuna rashin gamsuwa da tsarin zaɓen. Wani mamba daga Jekadafari, Adamu Sa’adu, ya zargi jami’an jam’iyyar da murɗe sakamakon zaɓen, yana mai cewa ba a gudanar da sahihin zaɓe ba.
Tun da farko APC a Gombe ta amince da tsarin sulhu wajen zaɓen ‘yan takara, amma wasu masu neman takara sukabƙi amince wa da hakan, lamarin da ya sa jam’iyyar ta koma tsarin zaɓen kai tsaye.















Discussion about this post