Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya yi alƙawarin bayar da tallafin gaggawa da kuma shirin mayar da mutanen da rikici ya raba da muhallansu zuwa garuruwansu tare da haɗin gwuiwar rundunar sojin Nijeriya.
Zulum ya bayyana hakan ne ranar Lahadi yayin ziyarar da ya kai sansanin ‘yan gudun hijira a Monguno, inda ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta dawo da martabar mutanen da rikicin tsaro ya shafa tare da tabbatar da komawarsu cikin aminci zuwa gidajensu na asali.
Yayin ganawarsa da iyalai da suka haɗa da mata, da yara da tsofaffi a sansanin ‘yan gudun hijira, gwamnan ya ce gwamnati tare da hukumomin tsaro sun amince da samar da tallafin gaggawa musamman a ɓangarorin ruwa, da matsuguni da kayan tsaftar muhalli.
“Gwamnati tare da shugabannin rundunar soji mun nazarci halin da ake ciki, kuma mun yanke shawarar samar da tallafin jin ƙai cikin gaggawa ga waɗannan al’ummomi musamman a ɓangarorin ruwa, da matsuguni da tsafta,” in ji Babagana Umara Zulum.
Ya ƙara da cewa gwamnati na tsara hanyoyin matsakaici da na dogon lokaci domin tabbatar da ɗorewar sake tsugunar da mutanen a garuruwansu. Gwamnan ya kuma buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanan sirri masu amfani, yana mai cewa tsaro alhakin kowa ne. Ya bayyana cewa sama da mutum 50,000 da suka dawo gida suna yankin Marte, yayin da ake shirye-shiryen ƙarin mayar da wasu a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin dawo da zaman lafiya.















Discussion about this post