ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Malami Sheikh Dahiru Usman

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi alhinin rasuwar babban malamin addinin Muslunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamba.

 

A saƙon ta’aziyya da ya fitar ta hannun mai magana da yawunsa Mukhtar Gidado, Gwamnan a madadin iyalansa, gwamanti da al’ummar jihar Bauchi, ya nuna matuƙar jimamin wannan babban rashin tare da miƙa ta’aziyya ga iyalansa marigayin, almajiransa, ɗalibai da ma al’ummar Musulmi a faɗin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya.

ADVERTISEMENT
  • Mbappe Ya Kafa Wani Sabon Tarihi A Gasar Zakarun Turai
  • Xi Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Ranar Nuna Goyon Baya Ga Palasdinawa Ta Duniya 

Ya ce, “Innalillahi wa inna ilaihirraji’un, cike da baƙin ciki da jimami na rashi, gwamnatin jihar Bauchi ta na sanar da rasuwar fitaccen malamin addinin musulunci, jagora, kuma babban shugaban addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya koma ga mahaliccinsa da sanyin safiyar yau Alhamis 27 ga watan Nuwamba 2025 a Bauchi yana da shekaru 102 a duniya.”

 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

A cewar Gwamna Bala Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya kasance jigo ne a fannin ilimin addinin Islama, mutum ne mai zurfin imani, kaskantar da kai, da hikima, tawali’u da sadaukar da kai domin addinin Musulunci, “Rayuwarsa ta duƙufa wajen yaɗa addinin Musulunci, karantar da Alƙur’ani mai girma, da kuma koyar da ɗabi’u da saita zukatan mutane bisa daidai.”

 

Ya ƙara da cewa ta hanyar kama Makarantu da daman gaske da cibiyoyin koyar da addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman ya ilmantar da dubban ɗalibai waɗanda suka haddadace Alƙur’ani mai girma da ilimin addinin Muslunci a fannoni daban daban a fadin Afrika.

 

Ya kuma nuna cewa irin salon koyarwar malamin na son zaman lafiya da ci gaban ƙasa hadi da neman haɗa kan jama’a ba za su misaltu ba, waɗanda za a ci gaba da tunawa da su tsawon shekaru.

 

Gwamna Bala Mohammed ya ce Babban rashi ne aka yi na jajirtaccen malami wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen bauta wa Allah da hidimarta masa da koyarwa da bada tarbiyya wa jama’a, “Tarihin rayuwasa zai cigaba da wanzuwa har al’ummar da za su nan gaba su yi koyi.”

 

Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar Bauchi za ta ci gaba da karrama shi da bada gudunmawa wa Cibiyoyin da ya bari domin ci gaba da kyautata ilimin addinin Musulunci da ɗa’a da cigaban al’umma.

 

Ya yi addu’ar Allah ya gafarta masa ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma jajanta wa iyalansa da almajiransa da al’ummar Musulmai.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Jajantawa Iyalan Mamatan Da Ibtila’in Gobara Ya Rutsa Da Su A Hong Kong 

Xi Jinping Ya Jajantawa Iyalan Mamatan Da Ibtila’in Gobara Ya Rutsa Da Su A Hong Kong 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.