ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Malami Sheikh Dahiru Usman

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi alhinin rasuwar babban malamin addinin Muslunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamba.

 

A saƙon ta’aziyya da ya fitar ta hannun mai magana da yawunsa Mukhtar Gidado, Gwamnan a madadin iyalansa, gwamanti da al’ummar jihar Bauchi, ya nuna matuƙar jimamin wannan babban rashin tare da miƙa ta’aziyya ga iyalansa marigayin, almajiransa, ɗalibai da ma al’ummar Musulmi a faɗin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya.

ADVERTISEMENT
  • Mbappe Ya Kafa Wani Sabon Tarihi A Gasar Zakarun Turai
  • Xi Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Ranar Nuna Goyon Baya Ga Palasdinawa Ta Duniya 

Ya ce, “Innalillahi wa inna ilaihirraji’un, cike da baƙin ciki da jimami na rashi, gwamnatin jihar Bauchi ta na sanar da rasuwar fitaccen malamin addinin musulunci, jagora, kuma babban shugaban addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya koma ga mahaliccinsa da sanyin safiyar yau Alhamis 27 ga watan Nuwamba 2025 a Bauchi yana da shekaru 102 a duniya.”

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A cewar Gwamna Bala Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya kasance jigo ne a fannin ilimin addinin Islama, mutum ne mai zurfin imani, kaskantar da kai, da hikima, tawali’u da sadaukar da kai domin addinin Musulunci, “Rayuwarsa ta duƙufa wajen yaɗa addinin Musulunci, karantar da Alƙur’ani mai girma, da kuma koyar da ɗabi’u da saita zukatan mutane bisa daidai.”

 

Ya ƙara da cewa ta hanyar kama Makarantu da daman gaske da cibiyoyin koyar da addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman ya ilmantar da dubban ɗalibai waɗanda suka haddadace Alƙur’ani mai girma da ilimin addinin Muslunci a fannoni daban daban a fadin Afrika.

 

Ya kuma nuna cewa irin salon koyarwar malamin na son zaman lafiya da ci gaban ƙasa hadi da neman haɗa kan jama’a ba za su misaltu ba, waɗanda za a ci gaba da tunawa da su tsawon shekaru.

 

Gwamna Bala Mohammed ya ce Babban rashi ne aka yi na jajirtaccen malami wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen bauta wa Allah da hidimarta masa da koyarwa da bada tarbiyya wa jama’a, “Tarihin rayuwasa zai cigaba da wanzuwa har al’ummar da za su nan gaba su yi koyi.”

 

Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar Bauchi za ta ci gaba da karrama shi da bada gudunmawa wa Cibiyoyin da ya bari domin ci gaba da kyautata ilimin addinin Musulunci da ɗa’a da cigaban al’umma.

 

Ya yi addu’ar Allah ya gafarta masa ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma jajanta wa iyalansa da almajiransa da al’ummar Musulmai.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Jajantawa Iyalan Mamatan Da Ibtila’in Gobara Ya Rutsa Da Su A Hong Kong 

Xi Jinping Ya Jajantawa Iyalan Mamatan Da Ibtila’in Gobara Ya Rutsa Da Su A Hong Kong 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.