ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Malami Sheikh Dahiru Usman

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi alhinin rasuwar babban malamin addinin Muslunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamba.

 

A saƙon ta’aziyya da ya fitar ta hannun mai magana da yawunsa Mukhtar Gidado, Gwamnan a madadin iyalansa, gwamanti da al’ummar jihar Bauchi, ya nuna matuƙar jimamin wannan babban rashin tare da miƙa ta’aziyya ga iyalansa marigayin, almajiransa, ɗalibai da ma al’ummar Musulmi a faɗin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya.

ADVERTISEMENT
  • Mbappe Ya Kafa Wani Sabon Tarihi A Gasar Zakarun Turai
  • Xi Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Ranar Nuna Goyon Baya Ga Palasdinawa Ta Duniya 

Ya ce, “Innalillahi wa inna ilaihirraji’un, cike da baƙin ciki da jimami na rashi, gwamnatin jihar Bauchi ta na sanar da rasuwar fitaccen malamin addinin musulunci, jagora, kuma babban shugaban addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya koma ga mahaliccinsa da sanyin safiyar yau Alhamis 27 ga watan Nuwamba 2025 a Bauchi yana da shekaru 102 a duniya.”

 

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

A cewar Gwamna Bala Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya kasance jigo ne a fannin ilimin addinin Islama, mutum ne mai zurfin imani, kaskantar da kai, da hikima, tawali’u da sadaukar da kai domin addinin Musulunci, “Rayuwarsa ta duƙufa wajen yaɗa addinin Musulunci, karantar da Alƙur’ani mai girma, da kuma koyar da ɗabi’u da saita zukatan mutane bisa daidai.”

 

Ya ƙara da cewa ta hanyar kama Makarantu da daman gaske da cibiyoyin koyar da addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman ya ilmantar da dubban ɗalibai waɗanda suka haddadace Alƙur’ani mai girma da ilimin addinin Muslunci a fannoni daban daban a fadin Afrika.

 

Ya kuma nuna cewa irin salon koyarwar malamin na son zaman lafiya da ci gaban ƙasa hadi da neman haɗa kan jama’a ba za su misaltu ba, waɗanda za a ci gaba da tunawa da su tsawon shekaru.

 

Gwamna Bala Mohammed ya ce Babban rashi ne aka yi na jajirtaccen malami wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen bauta wa Allah da hidimarta masa da koyarwa da bada tarbiyya wa jama’a, “Tarihin rayuwasa zai cigaba da wanzuwa har al’ummar da za su nan gaba su yi koyi.”

 

Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar Bauchi za ta ci gaba da karrama shi da bada gudunmawa wa Cibiyoyin da ya bari domin ci gaba da kyautata ilimin addinin Musulunci da ɗa’a da cigaban al’umma.

 

Ya yi addu’ar Allah ya gafarta masa ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma jajanta wa iyalansa da almajiransa da al’ummar Musulmai.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

MASU ALAKA

Bauchi
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bauchi
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Jajantawa Iyalan Mamatan Da Ibtila’in Gobara Ya Rutsa Da Su A Hong Kong 

Xi Jinping Ya Jajantawa Iyalan Mamatan Da Ibtila’in Gobara Ya Rutsa Da Su A Hong Kong 

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Bauchi

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bauchi

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.