Ƙungiyar Matasan Musulman Kudancin Kaduna (MYFOSKA) ta yi kira ga ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki a Jihar Kaduna da su guji amfani da addini da ƙabila wajen neman goyon bayan jama’a gabanin zaɓen shekarar 2027, tana mai cewa hakan na iya barazana ga zaman lafiya da haɗin kan al’ummar jihar.
A cikin wata sanarwa da Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Dakta K. Muhammed, ya sanya wa hannu, ya ce muhawarar da ta biyo bayan fitar da ‘yan takarar mataimakan gwamna na manyan jam’iyyun siyasa ta haifar da wasu kalamai da ke iya haddasa rarrabuwar kawuna tsakanin al’umma.
Ƙungiyar ta bayyana cewa matsayin Musulman Kudancin Kaduna ba ya nufin suna ƙin tsarin siyasar da ake da shi a yanzu, domin Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ‘yar asalin Kudancin Kaduna ce, kuma nadinta ya zama tarihi ga yankin.
MYFOSKA ta ce abin da ya kamata a fi mayar da hankali a kai shi ne tabbatar da adalci, bai wa kowa dama da kuma shugabanci mai haɗa kan al’umma ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.
Ta kuma yi gargaɗi kan yaɗa alkaluman yawan jama’a da ba su da tushe ko amfani da kalaman da za su iya tayar da fitina, tana mai jaddada cewa nasarar zaɓe ƙuri’un al’umma ne ke tabbatar da ita, ba ikirarin rinjayen wata ƙungiya ba.
Ƙungiyar ta buƙaci jam’iyyun siyasa da ‘yan takara su gudanar da yakin neman zaɓe bisa manufofi da shirye-shiryen ci gaban al’umma maimakon amfani da bambancin addini ko ƙabila wajen neman ƙuri’u.
MYFOSKA ta yi kira ga Musulman Kudancin Kaduna da sauran al’ummar jihar da su ci gaba da kasancewa masu bin doka, kiyaye zaman lafiya da kuma tabbatar da haɗin kai domin cigaban Jihar Kaduna da ƙasa baki ɗaya.














