Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar ƙananan hukumomin Birnin Gwari da Giwa, Hon. Bashir Zubairu Usman (Ciroman Birnin Gwari), ya sha alwashin cewa ba zai bari jinin mutanen da aka kashe a rikicin da ya shafi masu haƙar ma’adanai a yankin Randagi da ke ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna ya tafi a banza ba.
Hon. Bashir ya bayyana haka ne yayin wata tattaunawa da manema labarai a Kaduna, inda ya ce zai yi duk abin da ya dace domin tabbatar da cewa an yi wa waɗanda suka rasa rayukansu adalci kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce abin da ya faru ya tayar da hankali, yana mai jaddada cewa dole ne a gudanar da cikakken bincike domin gano hakikanin abin da ya faru tare da hukunta duk wanda aka samu da hannu a lamarin.
Ɗan majalisar ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci, tare da tabbatar da cewa ba a yi wa kowa son rai ba wajen gudanar da binciken.
A cewarsa, “Kamar yadda aka sani, yankin Birnin Gwari ya daɗe yana fama da matsalar hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa. Sai dai a wannan karon lamarin ya ɗauki wani sabon salo, inda ake zargin gamayyar jami’an tsaro na JTF da ƙaddamar da hari kan mutanen da ke aikin haƙar ma’adanai, lamarin da ya yi sanadin rasa rayuka masu yawa.”
Ya ƙara da cewa, “Wannan ba al’amari ba ne da za a bari ya wuce haka kawai. Dole ne a bi diddiginsa har sai an tabbatar da gaskiya kuma adalci ya yi aiki ga duk wanda abin ya shafa.”
Hon. Bashir Zubairu ya buƙaci gwamnati da hukumomin da abin ya shafa su ɗauki matakan da suka dace domin kauce wa sake faruwar irin wannan lamari a nan gaba, yana mai jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu tare da addu’ar Allah Ya jikansu da rahama.













