Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauke Buba Galadima daga muƙaminsa na Shugaban Majalisar Gudanarwar Kano Polytechnic, tare da naɗa Sarkin Gaya, Aliyu Ibrahim Abdulkadir, a matsayin wanda zai maye gurbinsa.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, an ce matakin na daga cikin sauye-sauyen da gwamnati ke yi domin inganta ayyukan makarantar.
- Tsadar Rayuwa Ta Sa Malamai Fara Aikin Wucin Gadi
- Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Samar Da Kundin Amfani Da Takin Zamani
Ko da yake wa’adin majalisar shekaru uku ne, gwamnati ta ce an kawo ƙarshen naɗin ne tun kafin cikar wa’adin domin daidaita shi da sabon tsarin gyare-gyaren da ake yi.
Gwamnan ya gode wa Galadima bisa gudummawar da ya bayar a lokacin da yake kan muƙamin.
Haka kuma, ya buƙaci sabon shugaban ya yi amfani da ƙwarewarsa wajen ƙarfafa ingancin karatu, inganta gudanarwa, da kuma tallafa wa ci gaban makarantar a ƙarƙashin shirin gyaran ilimi na gwamnati.















Discussion about this post