Gwamnan Jihar Sakkwato Ahmed Aliyu ya bayar da umurnin daukar malaman makarantar Ma’ahadut Tahfizi Waddarasatul Qur’aniyya 53 aiki a matsayin ma’aikatan gwamnatin jiha nan take.
Gwamnan ya umurci ma’aikatar lamurran addini da ta hada hannu da ma’aikatar kudi domin tabbatar da saka malaman a cikin tsarin albashi daga watan maris.
ADVERTISEMENT
Haka ma gwamnatin ta bayar da kyautar babura 259 ga daliban da suka haddace Alkur’ani a bikin yaye mahaddatan.
A cewar Gwamnan ba wai suna murnar kammala haddar Alqur’anin daliban ba ne kawai ba suna kuma murnar sadaukarwa, jajircewa ladabi da biyayya da himmatuwa ga koyarwar ubangiji.
-
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokotohttps://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
-
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokotohttps://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
-
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokotohttps://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
-
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokotohttps://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/















Discussion about this post