ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Za Ta Haramta Haihuwa Ba A Asibiti Ba

by Khalid Idris Doya
6 months ago
Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi na duba yiwuwar samar da doka ta musamman domin daƙile ƙaruwar yawan haihuwa a gida, lamarin da ke ƙara jefa lafiyar iyaye mata da jariransu a cikin haɗari.

Bisa alƙaluman da Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya wato UNICEF, ya fitar, ya ce kaso uku na mata ne kacal cikin kaso goma ke haihuwa a asibiti wato kaso 31 cikin 100. Yayin da sauran mata kaso bakwai, kwantankwacin kashi 69 cikin 100, su ke haihuwa a gida.

  • Xi Da Takwaransa Na Aljeriya Sun Taya Juna Murna Kan Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Aljeriya
  • Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan ISWAP, Sun Cafke Ƴan Fashi A Borno Da Adamawa

Game da duba lafiyar ciki wato antenatal, cikin mata 100 masu juna biyu, 57 ne suke zuwa antenatal amma daga bisani sukan haihu a gida.

ADVERTISEMENT

Masu ruwa da tsaki a harƙar kiwon lafiya sun nuna hakan a matsayin abun damuwa matuƙa inda suke kiran da a ɗauki matakin shawo kan hakan cikin hanzari.

Don haka ne ma’aikatar kula da lafiya a matakin farko ta jihar Bauchi, Majalisar Dokoki ta Jihar Bauchi, shugabannin ƙananan hukumomi da ƙungiyoyin fararen hula suka tsara hanyoyin rage yawaitar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Da ya ke jawabi a ranar Asabar a wajen taron tattaunawa na kwanaki biyu kan hanyoyin da za a bi wajen magance matsalar mace-macen masu juna biyu da jarirai da inganta kiwon lafiya uwa da jarirai, ƙwararren masani kan lafiya na UNICEF, Oluseyi Olosunde, ya ce yana da matukar muhimmanci masu ruwa da tsaki su nemo mafita domin rage mace-macen mata masu juna biyu da yara a jihar.

Ya buƙaci jihar da ta ƙara kasafin kuɗi wajen kula da kiwon lafiya. A cewarsa, alƙaluman da ake da su na buƙatar ɗaukar matakin gaggawa daga masu riƙe da madafun iko a jihar.

Shugaban hukumar kula da lafiyar a matakin farko ta Jihar Bauchi (BSPHDB), Dakta Rilwanu Muhammad, ya ce hukumar ta gano cewa mata da dama suna halartar antenatal amma daga bisani sukan zaɓi haihuwa a gida, lamarin da ke haifar da matsaloli tare da ƙara yawan mace-macen uwa da jariri a jihar.

“Mun yanke shawarar haɗa kowa da kowa, Kakakin Majalisar Dokoki da ’yan majalisa, masu tsara manufofi a ƙananan hukumomi da sauran su, domin duba batun kasafin kudi da sakin kuɗaɗe. Batun mace-macen uwa da jarirai abun damuwarmu ne.”

“A tsawon shekaru, kasafin kuɗinmu ya wuce yadda ma Abuja Declaration ta ayyana na kashi 15 cikin 100 ga lafiya, amma muna ɗaukar ƙarin matakai domin tabbatar da cewa hakan ya haifar da sakamakon mai kyau.

“Ɗaya daga cikin shawarwarin da aka bayar shi ne jihar ta samar da doka da za ta tilasta wa mata halartar antenatal da kuma haihuwa a cibiyoyin lafiya.

“Idan mace ta kasa halartar antenatal ko ta haihu a cibiyar lafiya, ya kamata a hukunta ta, ko ta hanyar tara mai tsauri ko ɗauri a kurkuku, domin tana jefa rayuwar ‘ya’yanta da nata cikin haɗari,” in ji shi.

Hakazalika, Dakta Nuzhat Rafique, babbar jami’ar da ke kula da ofishin UNICEF a Bauchi, ta ce idan aka kafa irin wannan doka, babu wanda zai hana mata zuwa antenatal ko haihuwa a asibiti.

Rafique, wadda ta nuna damuwa kan yawan mace-macen iyaye mata da jarirai a jihar.

Ta bayyana cewa UNICEF na aiki tare da masu ruwa da tsaki a ɓangaren lafiya, shugabannin gargajiya da na addini domin tabbatar da cewa mata sun san irin ayyukan lafiya da ya kamata su samu a lokacin ɗaukar ciki domin haihuwa lafiya, da kuma ayyukan bayan haihuwa wato raino da shayarwa.

Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Bauchi, Abubakar Suleiman, ya bayyana rashin jin daɗinsa da waɗannan alƙaluman lafiya, yana mai cewa bayanan suna nuna haƙiƙanin halin da ake ciki a jihar, tare da alwashin ƙarfafa aikin sa ido na majalisar domin tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin da lamarin ya rataya a wuyansu suna bayar da ingantaccen kulawar lafiya ga jama’a yadda ya dace.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Za A Wallafa Makalar Shugaba Xi Kan Bunkasa Karfin Samun Kudaden Kasar Sin

Za A Wallafa Makalar Shugaba Xi Kan Bunkasa Karfin Samun Kudaden Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.