ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Za Ta Haramta Haihuwa Ba A Asibiti Ba

by Khalid Idris Doya
7 months ago
Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi na duba yiwuwar samar da doka ta musamman domin daƙile ƙaruwar yawan haihuwa a gida, lamarin da ke ƙara jefa lafiyar iyaye mata da jariransu a cikin haɗari.

Bisa alƙaluman da Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya wato UNICEF, ya fitar, ya ce kaso uku na mata ne kacal cikin kaso goma ke haihuwa a asibiti wato kaso 31 cikin 100. Yayin da sauran mata kaso bakwai, kwantankwacin kashi 69 cikin 100, su ke haihuwa a gida.

  • Xi Da Takwaransa Na Aljeriya Sun Taya Juna Murna Kan Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Aljeriya
  • Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan ISWAP, Sun Cafke Ƴan Fashi A Borno Da Adamawa

Game da duba lafiyar ciki wato antenatal, cikin mata 100 masu juna biyu, 57 ne suke zuwa antenatal amma daga bisani sukan haihu a gida.

ADVERTISEMENT

Masu ruwa da tsaki a harƙar kiwon lafiya sun nuna hakan a matsayin abun damuwa matuƙa inda suke kiran da a ɗauki matakin shawo kan hakan cikin hanzari.

Don haka ne ma’aikatar kula da lafiya a matakin farko ta jihar Bauchi, Majalisar Dokoki ta Jihar Bauchi, shugabannin ƙananan hukumomi da ƙungiyoyin fararen hula suka tsara hanyoyin rage yawaitar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Da ya ke jawabi a ranar Asabar a wajen taron tattaunawa na kwanaki biyu kan hanyoyin da za a bi wajen magance matsalar mace-macen masu juna biyu da jarirai da inganta kiwon lafiya uwa da jarirai, ƙwararren masani kan lafiya na UNICEF, Oluseyi Olosunde, ya ce yana da matukar muhimmanci masu ruwa da tsaki su nemo mafita domin rage mace-macen mata masu juna biyu da yara a jihar.

Ya buƙaci jihar da ta ƙara kasafin kuɗi wajen kula da kiwon lafiya. A cewarsa, alƙaluman da ake da su na buƙatar ɗaukar matakin gaggawa daga masu riƙe da madafun iko a jihar.

Shugaban hukumar kula da lafiyar a matakin farko ta Jihar Bauchi (BSPHDB), Dakta Rilwanu Muhammad, ya ce hukumar ta gano cewa mata da dama suna halartar antenatal amma daga bisani sukan zaɓi haihuwa a gida, lamarin da ke haifar da matsaloli tare da ƙara yawan mace-macen uwa da jariri a jihar.

“Mun yanke shawarar haɗa kowa da kowa, Kakakin Majalisar Dokoki da ’yan majalisa, masu tsara manufofi a ƙananan hukumomi da sauran su, domin duba batun kasafin kudi da sakin kuɗaɗe. Batun mace-macen uwa da jarirai abun damuwarmu ne.”

“A tsawon shekaru, kasafin kuɗinmu ya wuce yadda ma Abuja Declaration ta ayyana na kashi 15 cikin 100 ga lafiya, amma muna ɗaukar ƙarin matakai domin tabbatar da cewa hakan ya haifar da sakamakon mai kyau.

“Ɗaya daga cikin shawarwarin da aka bayar shi ne jihar ta samar da doka da za ta tilasta wa mata halartar antenatal da kuma haihuwa a cibiyoyin lafiya.

“Idan mace ta kasa halartar antenatal ko ta haihu a cibiyar lafiya, ya kamata a hukunta ta, ko ta hanyar tara mai tsauri ko ɗauri a kurkuku, domin tana jefa rayuwar ‘ya’yanta da nata cikin haɗari,” in ji shi.

Hakazalika, Dakta Nuzhat Rafique, babbar jami’ar da ke kula da ofishin UNICEF a Bauchi, ta ce idan aka kafa irin wannan doka, babu wanda zai hana mata zuwa antenatal ko haihuwa a asibiti.

Rafique, wadda ta nuna damuwa kan yawan mace-macen iyaye mata da jarirai a jihar.

Ta bayyana cewa UNICEF na aiki tare da masu ruwa da tsaki a ɓangaren lafiya, shugabannin gargajiya da na addini domin tabbatar da cewa mata sun san irin ayyukan lafiya da ya kamata su samu a lokacin ɗaukar ciki domin haihuwa lafiya, da kuma ayyukan bayan haihuwa wato raino da shayarwa.

Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Bauchi, Abubakar Suleiman, ya bayyana rashin jin daɗinsa da waɗannan alƙaluman lafiya, yana mai cewa bayanan suna nuna haƙiƙanin halin da ake ciki a jihar, tare da alwashin ƙarfafa aikin sa ido na majalisar domin tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin da lamarin ya rataya a wuyansu suna bayar da ingantaccen kulawar lafiya ga jama’a yadda ya dace.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Za A Wallafa Makalar Shugaba Xi Kan Bunkasa Karfin Samun Kudaden Kasar Sin

Za A Wallafa Makalar Shugaba Xi Kan Bunkasa Karfin Samun Kudaden Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.