ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan ISWAP, Sun Cafke Ƴan Fashi A Borno Da Adamawa

by Abubakar Sulaiman
4 months ago
Sojoji

Sojojin rundunar Operation HAƊIN KAI (OPHK) sun samu gagarumar nasara a yankin Arewa maso Gabas, inda suka hallaka manyan jagororin ’yan ta’adda, suka kuma tarwatsa ayyukan ISWAP da Boko Haram, tare da daƙile wasu laifuka ta hanyar samun bayanan leƙen asiri da kai farmaki cikin tsari.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a Maiduguri, an tabbatar da hallaka Julaibib, wani babban kwamandan ISWAP da ke aiki a yankin Gujba na Timbuktu Triangle, a wata arangama da ta faru a kusa da Kimba, ƙaramar hukumar Damboa, a ranar Juma’a, 30 ga Janairu, 2026. Ya ce kisan jagoran ya jefa ’yan ISWAP cikin ruɗani, inda aka ce an kuma hallaka wasu daga cikinsu yayin farmakin.

  • Gwamnatin Jihar Borno Za Ta Dawo Da ‘Yan Gudun Hijira 3,000 Daga Kamaru
  • ’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa

Uba ya ƙara da cewa, a wani artabun na daban, sojoji tare da haɗin gwuiwar Civilian Joint Task Force (CJTF) sun yi kwanton ɓauna tsakanin Ngazalgana da Lamusheri a Jihar Borno, inda suka hallaka ’yan ta’adda uku. An ce sojojin sun yi amfani da bayanan sirri wajen kafa tarko a wata hanya, lamarin da ya sa suka yi nasara, tare da kwato bindigogi AK-47 guda biyu daga wajensu.

ADVERTISEMENT

A ranar 29 ga Janairu, 2026, sojoji sun kuma yi arangama da ’yan Boko Haram/ISWAP a Tsokorok, ƙaramar hukumar Gwoza, inda suka tilasta musu ja da baya bayan sun hallaka guda ɗaya daga cikinsu, tare da kwato babura guda biyu. A Adamawa kuma, sojoji sun amsa kiran gaggawa daga al’ummar Barama a Mubi North, inda suka dakile yunƙurin fashi, suka cafke mutane biyu da ke ƙoƙarin kai hari ga wani ɗalibi na Federal Polytechnic, Mubi, tare da ƙwato adda, da kwamfutoci tafi-da-gidanka, wayoyi da na’urar caji.

Hakazalika, a wani sintiri da aka yi tare da ’yan sa kai a hanyar Amtasa–Washim a ƙaramar hukumar Hong, sojoji sun fafata da ’yan ta’adda, suka tilasta musu guduwa, tare da ceto wata mata da aka sace. An kuma ƙwato bindigar AK-47 da harsasai da sauran makamai.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Sojoji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Wannan Wasika Ta Bayyana Kaunar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Wannan Wasika Ta Bayyana Kaunar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.