ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Ce Shari’ar Zidan Ta Gudana Cikin Gaskiya da Adalci

by Shehu Yahaya and Sulaiman
5 months ago
Kotu

Gwamnatin Jihar Kaduna ta jaddada cewa an bi dukkan ka’idojin shari’a yadda ya dace, bisa hujjoji da shaidu na gaskiya inda ta karyata rahotonin kafafen sada zamunta dangane yanke hukuncin kisa da aka yanke wa Zidan.

 

Da yake jawabi kan ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan hukuncin da kotu ta yanke a ranar 6 ga Janairu, 2026, Kwamishinan Shari’a, James A. Kanyip, ya bayyana cewa Victor Solomon wanda akafi sani da Zidan ya fuskanci shari’u guda biyu daban-daban a gaban kotuna biyu mabambanta, kan laifuffuka daban-daban da suka shafi mutane daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 3 Da Abubuwan Fashewa A Katsina
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 3 Da Abubuwan Fashewa A Katsina

A wata sanarwa da rabawa manema labarai Kwamishinan yace “Babu wani sabani a hukuncin da ake ta yadawa a kafafen sada zumunta.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Victor Solomon an gurfanar da shi ne a shari’u biyu daban. An wanke shi daga zargi a shari’a guda a shekarar 2024, amma kuma an same shi da laifi a wata shari’ar daban a 2026 bisa ga shaidu da aka gabatar a kotu,” in ji Kanyip.

 

Ya bayyana cewa shari’a ta farko mai Lamba KDH/KAD/73C/2020 wadda ta shafi haɗa baki wajen aikata laifi da yunƙurin aikata kisan kai, ta ƙare da sallamar sa tare da wanke shi daga zargi a ranar 21 ga Mayu, 2024”

 

“Shari’a ta biyu mai Lamba KDH/KAD/78C/202 ta shafi manyan laifuffuka da suka haɗa da haɗa baki wajen aikata laifi, jikkata mutum ba tare da dalili ba, da kuma kisan kai da ke da hukuncin kisa. An kammala sauraron wannan shari’a a watan Oktoba, 2025, inda daga bisani aka same shi da laifi tare da yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya a ranar 6 ga Janairu, 2026.

 

“Kotun ba ta yanke hukunci bisa son rai ko dalilan siyasa ba. An bi doka da oda, an gudanar da cikakkiyar shari’a, kuma alkalin kotu ya tantance hujjoji da shaidu yadda ya dace,” in ji Kanyip

 

Ya ƙara da cewa wanda aka yanke wa hukunci yana da ‘yancin daukaka ƙara har zuwa Kotun Koli kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

 

Da Yake Karin haske kan hukuncin kotun , Kwamishinan Yada Labarai, Malam Ahmed Maiyaki, ya gargaɗi jama’a kan yaɗa labaran ƙarya musamman a kan muhimman batutuwan shari’a.

 

“Yaɗa labaran ƙarya game da hukuncin kotu abu ne mai hatsari. Yana iya tayar da hankalin jama’a da haddasa rikici ba tare da dalili ba. Muna kira ga al’ummar Kaduna da su rika tantance sahihancin labari kafin yadawa,” in ji Maiyaki.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna
Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Yawan Motoci Masu Aiki Da Sabbin Makamashi Da Sin Ta Sayar Ya Ci Gaba Da Zama Matsayin Farko A Duniya A 2025

Yawan Motoci Masu Aiki Da Sabbin Makamashi Da Sin Ta Sayar Ya Ci Gaba Da Zama Matsayin Farko A Duniya A 2025

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.