Gwamnatin Jihar Kano ta haɗe Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi zuwa ma’aikata guda.
Sabuwar ma’aikatar za ta riƙa aiki da sunan Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi.
Kwamishinan ma’aikatar, Dahir M. Hashim, ne ya sanar da hakan a ranar Litinin, inda ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da haɗewar.
Hashim ya gode wa gwamnan bisa ba shi amanar jagorantar sabuwar ma’aikatar.
Ya ce haɗe waɗannan muhimman ɓangarori biyu aiki ne da ke buƙatar jajircewa, haɗin kai da kuma kyakkyawan tsari.
Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa ma’aikatar a shirye take domin tabbatar da sauyi cikin sauƙi tare da inganta ayyuka a ɓangarorin biyu.
A cewarsa, ma’aikatar za ta ci gaba da mayar da hankali kan kare muhalli, tunkarar matsalolin sauyin yanayi da kuma inganta yadda ake sarrafa albarkatun ruwa, daidai da manufofin ci gaban gwamnatin Abba Kabir Yusuf.















Discussion about this post