Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa Gwamnatin Jihar Kano ta rubuta wa Gwamnatin Tarayya wasiƙa domin hana jagoran jam’iyyar, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, shigowa jihar Kano.
Galadima ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin wata hira da ya yi da DCL Hausa.
- Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban Hukumar Alhazai Ta Ƙasa Ambasada Ismail Abba Yusuf
- Shirin Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Na Kasar Sin: Da Sanyin Safiya Ake Kama Fara
Ya ce suna da masaniya kan wasiƙar kuma suna jiran martanin Gwamnatin Tarayya.
Ya tambayi dalilin da zai sa a hana Kwankwaso zuwa jiharsa, yana mai cewa za su kai ƙara kotu idan hakan ta zama dole.
Galadima ya kuma ƙaryata rahotannin da ke cewa Majalisar Dokokin Amurka na shirin sanya wa Kwankwaso takunkumin hana shi biza bisa zargin tsangwamar Kiristoci.
Ya ce zargin ba shi da tushe face siyasa ce kawai.
A cewarsa, wasu a cikin gwamnatin APC ba su ji daɗin yadda Kwankwaso ya ƙi komawa jam’iyyarsu ba.
Ya ce Kwankwaso ya tsaya kan matsayinsa, kuma ba zai shiga wata jam’iyya ba sai idan hakan zai amfani jama’a, ba don son rai ba.
Galadima ya kuma ce an yi barazanar kama shi da kuma ɓata masa suna ta hanyar ƙirƙirar zarge-zarge na ƙarya, amma ya ce Kwankwaso ba shi tsoro.
Ya ƙara da cewa NNPP za ta yanke shawarar makomarta gabanin zaɓen 2027 bisa abin da ya fi dacewa da magoya bayanta da kuma ‘yan Nijeriya baki ɗaya.















Discussion about this post