ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Ta Kare Shirinta Na Sakin Ƴan Ta’adda 70 Daga Gidan Yari

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana dalilin shirinta na sakin wasu mutane 70 da ke fuskantar shari’a, bisa zarginsu da hannu a ayyukan ta’addanci, inda ta bayyana hakan a matsayin wani yunƙuri na ƙarfafa yarjejeniyar zaman lafiya da ƙungiyoyin ƴan ta’addan a faɗin jihar.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Nasir Muazu, ya ce; an ɗauki matakin ne da nufin ɗorewar yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma tsakanin al’ummomin da abin ya shafa da kuma ƴan bindigar da suka tuba.

  • Shugabannin Ƙasashe Huɗu Da Amurka Ta Kama Amurka Ta Gurfanar Da shugaban Ɓenezuela Nicolas Maduro
  • Sakin Ƴan Bindiga 70 A Jihar Katsina: Ya Haifar Da Cece-kuce

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da gidan rediyon DCL Hausa, a ranar Asabar da ta gabata a daidai lokacin da jama’a ke nuna ɓacin ransu, kan wata wasiƙa da gwamnati ta fitar na neman a sa baki a shari’a domin a sako waɗanda ake tuhuma a halin yanzu.

ADVERTISEMENT

Ya ce, yarjejeniyar zaman lafiya ta yi sanadin sako mutane kusan 1,000 da aka yi garkuwa da su.

A cewar kwamishinan, aƙalla ƙananan hukumomi 15 ne suka shiga shirin samar da zaman lafiya, wanda a cewarsa; hakan ya sa aka sako mutane kusan 1,000 da aka sace.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Muazu ya kwatanta sakin waɗanda ake zargin da abin da ke faruwa a lokacin yaƙi, inda ɓangarorin da ke faɗa da juna ke musayar fursunoni.

Ma’aikatar shari’a ta Jihar Katsina ce ta fitar da wasiƙar, wadda Sahara Reporters ta fara aikowa da ita zuwa ga babban alƙalin jihar, inda ta buƙaci kwamitin da ke sa ido kan shari’a na manyan laifuffuka (ACJMC) ya sa baki, domin a sako waɗanda ake zargin.

Wasiƙar mai ɗauke da sa hannun Daraktan Ƙararrakin Jama’a Abdurrahman Umar, ta bayyana cewa; ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida ta miƙa jerin sunayen mutane 48 da ake zargi da laifuka daban-daban da suka shafi ta’addanci zuwa ma’aikatar shari’a.

Ma’aikatar ta ce, sakin da aka gabatar shi ne ya zama “ɗaya daga cikin sharuɗɗan ci gaba da yarjejeniyar zaman lafiya da aka rattabawa hannu tsakanin ƙananan hukumomi na gaba da ƴan ta’addar.”

Wasiƙar ta kuma bayyana cewa, yayin da aka gurfanar da wasu daga cikin waɗanda ake zargin a gaban babbar kotun tarayya, yawancinsu na ci gaba da tsare a kotunan majistare daban-daban na jihar, suna jiran shari’a.

Har ila yau, an kuma gabatar da jerin sunayen fursunoni kusan 22 da ke fuskantar shari’a a gaban manyan kotuna daban-daban na Jihar Katsina, domin a sake su a ƙarƙashin wannan shirin na zaman lafiya.

Kazalika, Ma’aikatar ta yi kira ga Babban Alƙalin Jihar da ya ɗauki matakin da ya dace, inda ta bayar da misali da sashe na 371(2) na dokar gudanar da shari’ar laifuka ta Jihar Katsina, 2021, wanda ya bayyana ikon kwamitin da ke sa ido kan shari’a.

Yayin da yake kare matakin sakin ƴan ta’addan kimanin 70, Muazu ya ce; yarjejeniyar zaman lafiya ta haifar da sakamako mai matuƙar ma’ana, musamman wajen sako mutanen da aka sace.

Ya ba da misali da alƙaluman waɗanda aka sako daga ƙananan hukumomin da suka haɗa da Sabuwa (310), Bakori (125), Danmusa (60), Dutsinma (62) da Safana (36).

Bugu da ƙari, Kwamishinan ya bayyana cewa; ma’aikatar shari’a ko kotuna, ba su taka wata doka da ake da ita ba, yana mai cewa; duk wanda bai gamsu da hukuncin ba, yana da ƴancin neman haƙƙinsa.

“A duk faɗin duniya, bayan yaƙe-yaƙe, ana yin musayar fursunoni, a lokacin yaƙin basasar Nijeriya, an yi musayar fursunoni, kamar yadda ya faru a tattaunawar da ta shafi Boko Haram.

“Batun ba wai ko batun an aikata wani laifi ko a’a ba, illa kawai tabbatar da zaman lafiya. musayar fursunoni ba wani sabon abu ba ne a tarihin yaƙi da zaman lafiya,” in ji shi.

Sunayen Ƴan Ta’addar Da Za A Saka

Wani jerin sunayen da jaridar Katsina Times, wata jarida ta yanar gizo a jihar ta samu, ya nuna cewa; akwai mata a cikin ƴan ta’adda 70 da za a sako.

Wasu daga cikin sunayen, akwai Hadiza Dije Hauwa’u daga Safana, Gambo Zubairu Faskari, Muntari Yusuf Safana, Yakubu Alhaji Ardo, Tukur Amadu (Liman), İdi Salisu Gaddi, Abdulhayatu Jabiru, Ya’u Buhari da Amadu Rufa’i Anare.

 

Dole Ne Gwamnati Ta Biya Iyalan Waɗanda Abin Ya Shafa

Da yake zantawa da jaridar Daily Trust ta wayar tarho, shugaban ƙungiyar ‘Network for Justice’, Abdullahi Hassan Kofar Sauri ya ce, ya kamata gwamnati ta biya diyya ga iyalan waɗanda harin ƴan bindiga ya shafa a jihar.

Ya ce, abin takaici ne yadda Gwamnatin Jihar Katsina da gwamnatin tarayya suka nuna cewa, ba su da hannu wajen tattaunawa da ƴan bindiga.

“Gwamnatin jihar na ƙoƙarin ganin ta saki wasu ƴan ta’adda da aka kama suke fuskantar shari’a a gaban kotu, wannan abu ne da gwamnatin jihar ta ce; ba ta da hannu a ciki, yanzu kuma waɗannan mutanen suna hannunsu.

“Ƴan ta’addan da aka yankewa hukuncin, suna hannun gwamnati, don haka; gwamnati na tsare da su, sannan kuma dole ne a yanke musu hukunci daban-daban.

“Kawai sai ga labarin cewa, an saki kusan 70 daga cikinsu, wannan lamari ne mai matuƙar tayar da hankali, wanda ya sanya mutane da dama cikin damuwa, sai na yi mamaki: me yasa yanzu gwamnatin jihar ta dawo tana cewa; za ta sake su?

“An yanke wa wani laifin kisan kai da ƙona-ƙone, a nan kuma yaya za ka yi da iyalan waɗanda aka kashe, ta wace hanya za ka biya su, shin gwamnatin jihar za ta fito ta ce, tunda mun saki wancan ɗan ta’addan da ya lalata maka gidanka ko ya kashe maka mahaifanka, yanzu za mu ba ka diyyar da ta dace, gwargwadon waɗanda abin ya shafa?

“Amma babu wanda ya ce komai game da lamarin, kuma waɗannan ƴan ta’adda da aka yanke wa hukunci da za a sako za su koma ƙauyuka, dazuzzuka tare da jama’ar yankin, ta yaya za ku daidaita tsakaninsu hakan? Shi ya sa mutane ke nuna shakku da damuwa.”

 

Sakin Waɗannan Ƴan Ta’adda Na Da Matuƙar Haɗari – Masanin tsaro

Wani masani kan harkokin tsaro, Yahuza Getso, a wata tattaunawa da aka yi da shi, ya bayyana matakin sakin ƴan bindigar a matsayin wata babbar barazana da kuma haɗari ga Jihar Katsina da ma ƙasa baki-ɗaya, inda ya ce; babu wanda zai iya aminta da su.

A cewar tasa, matakin babu gaskiya a cikinsa.

Ya ci gaba da cewa, “Akwai wani gwamna mai ci a halin yanzu daga yankin Arewa-maso-yamma, wanda kwanan nan ya raba babura ashirin da biyar ga ƴan ta’adda, yanzu ku gaya min ina batun gaskiya da jajircewa wajen kawo ƙarshen wannan matsala ta rashin tsaro?

Dawowar Hare-haren Ƴan Bindiga

Matakin da gwamnatin jihar ta ɗauka na ganin an sako ƴan bindiga 70, na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a jihar.

A ranar Litinin da ta gabata ne, wasu ƴan bindiga suka kai farmaki a wasu ƙauyukan Ƙaramar Hukumar Malumfashi da ke jihar, inda suka kashe mutane takwas tare da yin garkuwa da wasu da dama.

Ƙauyukan da abin ya shafa, sun haɗa da Unguwar Alhaji Barau, Gidan Dan Mai-gizo da Gidan Hazo.

Ya zuwa watan Nuwambar shekarar da ta gabata, ƙananan hukumomi 18 daga cikin 34 na jihar, sun ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya da ƴan bindiga.

Yayin da wasu daga cikin ƙananan hukumomin suka samu kwanciyar hankali, wasu kuma na ci gaba da fuskantar hare-hare, duk da tattaunawar da aka yi, lamarin da ya sanya ayar tambaya game da ingancin yarjejeniyar.

Ƙananan hukumomi 18 da suka shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ƴan bindigar sun haɗa da; Kankara, Kafur, Malumfashi, Funtua, Batagarawa, Charanchi, Sabuwa, Dandume, Faskari, Matazu, Musawa, Safana, Kurfi, Dutsinma, Jibia, Batsari, Danmusa da Bakori.

A ƙarƙashin yarjejeniyar, shugabannin al’umma da sarakunan gargajiya, sun yi alƙawarin mutunta sharuɗɗan, yayin da ƴan bindigar suka amince da dakatar da kai hare-hare, tare da sakin waɗanda aka kama.

Katsina
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Katsina

Asarar Naira Biliyan 10.16 A Noman Bara: Manoma A Kaduna Sun Buƙaci Ɗaukin Gaggawa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.