ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Naira Biliyan 10.16 A Noman Bara: Manoma A Kaduna Sun Buƙaci Ɗaukin Gaggawa

by Abubakar Abba
5 months ago
Noman

Manoma kimanin 2,143 a Jihar Kaduna, sun yi kira ga gwamnatin tarayya, da ta gaggauta kawo musu ɗauki, musamman ta fuskar ba su kayan aikin noma kyauta, ko kuma sayar musu da kayan a kan farashi mai sauƙi.

Sun yi wannan kira ne, biyo bayan mummunar asarar da suka tafka a kakar noman bara, wadda ta kai ta kimanin sama da naira biliyan 10.

  • Asusun NADF Ya Tallafa Wa Manoman Albasa 2,000 A Wasu Jihohin Kasar Nan
  • Ƙungiyar Manoma Na Neman Gwamnati Ta Tallafa Mata Da Kayan Aikin Noman Rani

Kiran nasu dai, na ƙunshe ne cikin wata takardar wasiƙa da suka rubuta tare da aikewa zuwa ofishin sakataren gwanatin tarayya da babban ministan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da gwamnan babban bankin Nijeriya da  kuma sanatoci uku da ke wakiltar Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, manoman waɗanda suka kasance sun fito ne daga shiyoyi uku na Kaduna, sun kuma koka a kan  faɗuwar da farashin Masara ya yi ɓagatatan, a dukkanin ɗaukacin faɗin wannan kasa, tare da kuma samun ƙarin farashin kayayyakin noma.

Manoman, sun rubuta wasiƙar ce ta hannun lauyansu, Barista Ehizogie Fidelis Imadojemu, wadda ke nuna cewa; manoman na gudanar da nomansu ne a ƙarƙashin shirin noman Masara, wanda Alhaji Rufai Muazu Dikko, da aka fi sani da Sarkin Labar, ke sanya ido.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Har ila yau, manoman sun ce; bisa wannan asarar da suka tabka, hakan ya sanya sun gaza mayar da kuɗaɗen da suka kashe, bayan sun yi girbi a kakar noman ta bara.

Suka ƙara da cewa, an faro shirin aikin noman ne, tun a shekarar 2017, wanda aka fara da kadadar noma kimanin  1,000, daga baya kuma aka faɗaɗa shirin zuwa kadada 10,000, inda aka noma kadada dubu 2,143 a Ƙananan Hukumomin Igabi, Soba, Kauru, Zariya da kuma Sabon Gari.

A cewarsu, a ƙarƙashin yarjejeniyar da aka ƙulla, Sarkin Labar ne ya samar da kuɗi da kuma kayan aiki, wanda kuma manoman idan sun yi girbi za su biya da Masara su kuma sayar da sauran abin da suka samu.

Haka zalika, sun bayyana cewa; buhun taki na NPK mai nauyin kilo 50, ana sayar da shi ne a kan kimanin naira 60,000, inda kuma na Urea, farashinsa ya ƙaru zuwa naira 50,000.

Sun ƙara da cewa, wannan dalili ne yasa jimillar kuɗin da suka kashe wajen noman kadada ɗaya ta Masara, kuɗin ya ƙaru zuwa sama da naira miliyan biyu daga naira miiyan ɗaya a bara.  

Manoman sun yi gargaɗin cewa, idan har mahukuntan wannan ƙasa, ba su kawo musu ɗaukin gaggawa ba, ko shakka babu; manoma da dama a Nijeriya, musamman a yankunan Arewa, ba za su iya yin noma a kakar noma ta bana ba.

Kazalika, sun buƙaci babban bankin Nijeriya (CBN), ya samar musu da ɗauki na rage farashin kayan aikin noma da takin zamani, samfurin urea da za su yi amfani da shi a kakar noman ta bana.

A cewarsu, idan babban bankin Nijeriya ya kawo musu ɗauki, su kuma za su biya bankin da wani kaso na Masarar da suka noma, wadda za ta yi daidai da ɗaukin da bankin ya ba su, bayan sun girbe amfanin nasu a kakar ta bana.

Manoman sun kuma bayyana cewa, samar musu da ɗaukin; zai taimaka musu matuƙa wajen sayen amfanin gona a cikin farashi mai rahusa da ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar da kuma ƙara bunƙasa tattalin arziƙin ƙasar, musamman duba da cewa; zaɓukan 2027 na ƙara ƙaratowa nan da ɗan ƙanƙanin lokaci.

Don haka, a cewar tasu; hakan ne kawai zai ba su damar komawa gonakinsu a kakar ta bana, domin ci gaba da noma gonakin nasu.

Kazalika, sun kuma buƙaci son tattaunawa da jami’an gwamnati, domin samun damar tunkarar noman na kakar ta bana.

Noman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Noman

Jiragen Ruwa Guda 32 Ɗauke Da Kaya Sun Sauka A Tashar Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.