ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Naira Biliyan 10.16 A Noman Bara: Manoma A Kaduna Sun Buƙaci Ɗaukin Gaggawa

by Abubakar Abba
5 months ago
Noman

Manoma kimanin 2,143 a Jihar Kaduna, sun yi kira ga gwamnatin tarayya, da ta gaggauta kawo musu ɗauki, musamman ta fuskar ba su kayan aikin noma kyauta, ko kuma sayar musu da kayan a kan farashi mai sauƙi.

Sun yi wannan kira ne, biyo bayan mummunar asarar da suka tafka a kakar noman bara, wadda ta kai ta kimanin sama da naira biliyan 10.

  • Asusun NADF Ya Tallafa Wa Manoman Albasa 2,000 A Wasu Jihohin Kasar Nan
  • Ƙungiyar Manoma Na Neman Gwamnati Ta Tallafa Mata Da Kayan Aikin Noman Rani

Kiran nasu dai, na ƙunshe ne cikin wata takardar wasiƙa da suka rubuta tare da aikewa zuwa ofishin sakataren gwanatin tarayya da babban ministan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da gwamnan babban bankin Nijeriya da  kuma sanatoci uku da ke wakiltar Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, manoman waɗanda suka kasance sun fito ne daga shiyoyi uku na Kaduna, sun kuma koka a kan  faɗuwar da farashin Masara ya yi ɓagatatan, a dukkanin ɗaukacin faɗin wannan kasa, tare da kuma samun ƙarin farashin kayayyakin noma.

Manoman, sun rubuta wasiƙar ce ta hannun lauyansu, Barista Ehizogie Fidelis Imadojemu, wadda ke nuna cewa; manoman na gudanar da nomansu ne a ƙarƙashin shirin noman Masara, wanda Alhaji Rufai Muazu Dikko, da aka fi sani da Sarkin Labar, ke sanya ido.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Har ila yau, manoman sun ce; bisa wannan asarar da suka tabka, hakan ya sanya sun gaza mayar da kuɗaɗen da suka kashe, bayan sun yi girbi a kakar noman ta bara.

Suka ƙara da cewa, an faro shirin aikin noman ne, tun a shekarar 2017, wanda aka fara da kadadar noma kimanin  1,000, daga baya kuma aka faɗaɗa shirin zuwa kadada 10,000, inda aka noma kadada dubu 2,143 a Ƙananan Hukumomin Igabi, Soba, Kauru, Zariya da kuma Sabon Gari.

A cewarsu, a ƙarƙashin yarjejeniyar da aka ƙulla, Sarkin Labar ne ya samar da kuɗi da kuma kayan aiki, wanda kuma manoman idan sun yi girbi za su biya da Masara su kuma sayar da sauran abin da suka samu.

Haka zalika, sun bayyana cewa; buhun taki na NPK mai nauyin kilo 50, ana sayar da shi ne a kan kimanin naira 60,000, inda kuma na Urea, farashinsa ya ƙaru zuwa naira 50,000.

Sun ƙara da cewa, wannan dalili ne yasa jimillar kuɗin da suka kashe wajen noman kadada ɗaya ta Masara, kuɗin ya ƙaru zuwa sama da naira miliyan biyu daga naira miiyan ɗaya a bara.  

Manoman sun yi gargaɗin cewa, idan har mahukuntan wannan ƙasa, ba su kawo musu ɗaukin gaggawa ba, ko shakka babu; manoma da dama a Nijeriya, musamman a yankunan Arewa, ba za su iya yin noma a kakar noma ta bana ba.

Kazalika, sun buƙaci babban bankin Nijeriya (CBN), ya samar musu da ɗauki na rage farashin kayan aikin noma da takin zamani, samfurin urea da za su yi amfani da shi a kakar noman ta bana.

A cewarsu, idan babban bankin Nijeriya ya kawo musu ɗauki, su kuma za su biya bankin da wani kaso na Masarar da suka noma, wadda za ta yi daidai da ɗaukin da bankin ya ba su, bayan sun girbe amfanin nasu a kakar ta bana.

Manoman sun kuma bayyana cewa, samar musu da ɗaukin; zai taimaka musu matuƙa wajen sayen amfanin gona a cikin farashi mai rahusa da ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar da kuma ƙara bunƙasa tattalin arziƙin ƙasar, musamman duba da cewa; zaɓukan 2027 na ƙara ƙaratowa nan da ɗan ƙanƙanin lokaci.

Don haka, a cewar tasu; hakan ne kawai zai ba su damar komawa gonakinsu a kakar ta bana, domin ci gaba da noma gonakin nasu.

Kazalika, sun kuma buƙaci son tattaunawa da jami’an gwamnati, domin samun damar tunkarar noman na kakar ta bana.

Noman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Noman

Jiragen Ruwa Guda 32 Ɗauke Da Kaya Sun Sauka A Tashar Jihar Legas

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.