ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Naira Biliyan 10.16 A Noman Bara: Manoma A Kaduna Sun Buƙaci Ɗaukin Gaggawa

by Abubakar Abba
6 months ago
Noman

Manoma kimanin 2,143 a Jihar Kaduna, sun yi kira ga gwamnatin tarayya, da ta gaggauta kawo musu ɗauki, musamman ta fuskar ba su kayan aikin noma kyauta, ko kuma sayar musu da kayan a kan farashi mai sauƙi.

Sun yi wannan kira ne, biyo bayan mummunar asarar da suka tafka a kakar noman bara, wadda ta kai ta kimanin sama da naira biliyan 10.

  • Asusun NADF Ya Tallafa Wa Manoman Albasa 2,000 A Wasu Jihohin Kasar Nan
  • Ƙungiyar Manoma Na Neman Gwamnati Ta Tallafa Mata Da Kayan Aikin Noman Rani

Kiran nasu dai, na ƙunshe ne cikin wata takardar wasiƙa da suka rubuta tare da aikewa zuwa ofishin sakataren gwanatin tarayya da babban ministan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da gwamnan babban bankin Nijeriya da  kuma sanatoci uku da ke wakiltar Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, manoman waɗanda suka kasance sun fito ne daga shiyoyi uku na Kaduna, sun kuma koka a kan  faɗuwar da farashin Masara ya yi ɓagatatan, a dukkanin ɗaukacin faɗin wannan kasa, tare da kuma samun ƙarin farashin kayayyakin noma.

Manoman, sun rubuta wasiƙar ce ta hannun lauyansu, Barista Ehizogie Fidelis Imadojemu, wadda ke nuna cewa; manoman na gudanar da nomansu ne a ƙarƙashin shirin noman Masara, wanda Alhaji Rufai Muazu Dikko, da aka fi sani da Sarkin Labar, ke sanya ido.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Har ila yau, manoman sun ce; bisa wannan asarar da suka tabka, hakan ya sanya sun gaza mayar da kuɗaɗen da suka kashe, bayan sun yi girbi a kakar noman ta bara.

Suka ƙara da cewa, an faro shirin aikin noman ne, tun a shekarar 2017, wanda aka fara da kadadar noma kimanin  1,000, daga baya kuma aka faɗaɗa shirin zuwa kadada 10,000, inda aka noma kadada dubu 2,143 a Ƙananan Hukumomin Igabi, Soba, Kauru, Zariya da kuma Sabon Gari.

A cewarsu, a ƙarƙashin yarjejeniyar da aka ƙulla, Sarkin Labar ne ya samar da kuɗi da kuma kayan aiki, wanda kuma manoman idan sun yi girbi za su biya da Masara su kuma sayar da sauran abin da suka samu.

Haka zalika, sun bayyana cewa; buhun taki na NPK mai nauyin kilo 50, ana sayar da shi ne a kan kimanin naira 60,000, inda kuma na Urea, farashinsa ya ƙaru zuwa naira 50,000.

Sun ƙara da cewa, wannan dalili ne yasa jimillar kuɗin da suka kashe wajen noman kadada ɗaya ta Masara, kuɗin ya ƙaru zuwa sama da naira miliyan biyu daga naira miiyan ɗaya a bara.  

Manoman sun yi gargaɗin cewa, idan har mahukuntan wannan ƙasa, ba su kawo musu ɗaukin gaggawa ba, ko shakka babu; manoma da dama a Nijeriya, musamman a yankunan Arewa, ba za su iya yin noma a kakar noma ta bana ba.

Kazalika, sun buƙaci babban bankin Nijeriya (CBN), ya samar musu da ɗauki na rage farashin kayan aikin noma da takin zamani, samfurin urea da za su yi amfani da shi a kakar noman ta bana.

A cewarsu, idan babban bankin Nijeriya ya kawo musu ɗauki, su kuma za su biya bankin da wani kaso na Masarar da suka noma, wadda za ta yi daidai da ɗaukin da bankin ya ba su, bayan sun girbe amfanin nasu a kakar ta bana.

Manoman sun kuma bayyana cewa, samar musu da ɗaukin; zai taimaka musu matuƙa wajen sayen amfanin gona a cikin farashi mai rahusa da ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar da kuma ƙara bunƙasa tattalin arziƙin ƙasar, musamman duba da cewa; zaɓukan 2027 na ƙara ƙaratowa nan da ɗan ƙanƙanin lokaci.

Don haka, a cewar tasu; hakan ne kawai zai ba su damar komawa gonakinsu a kakar ta bana, domin ci gaba da noma gonakin nasu.

Kazalika, sun kuma buƙaci son tattaunawa da jami’an gwamnati, domin samun damar tunkarar noman na kakar ta bana.

Noman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Noman

Jiragen Ruwa Guda 32 Ɗauke Da Kaya Sun Sauka A Tashar Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.