ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Naira Biliyan 10.16 A Noman Bara: Manoma A Kaduna Sun Buƙaci Ɗaukin Gaggawa

by Abubakar Abba
8 months ago
Noman

Manoma kimanin 2,143 a Jihar Kaduna, sun yi kira ga gwamnatin tarayya, da ta gaggauta kawo musu ɗauki, musamman ta fuskar ba su kayan aikin noma kyauta, ko kuma sayar musu da kayan a kan farashi mai sauƙi.

Sun yi wannan kira ne, biyo bayan mummunar asarar da suka tafka a kakar noman bara, wadda ta kai ta kimanin sama da naira biliyan 10.

  • Asusun NADF Ya Tallafa Wa Manoman Albasa 2,000 A Wasu Jihohin Kasar Nan
  • Ƙungiyar Manoma Na Neman Gwamnati Ta Tallafa Mata Da Kayan Aikin Noman Rani

Kiran nasu dai, na ƙunshe ne cikin wata takardar wasiƙa da suka rubuta tare da aikewa zuwa ofishin sakataren gwanatin tarayya da babban ministan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da gwamnan babban bankin Nijeriya da  kuma sanatoci uku da ke wakiltar Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, manoman waɗanda suka kasance sun fito ne daga shiyoyi uku na Kaduna, sun kuma koka a kan  faɗuwar da farashin Masara ya yi ɓagatatan, a dukkanin ɗaukacin faɗin wannan kasa, tare da kuma samun ƙarin farashin kayayyakin noma.

Manoman, sun rubuta wasiƙar ce ta hannun lauyansu, Barista Ehizogie Fidelis Imadojemu, wadda ke nuna cewa; manoman na gudanar da nomansu ne a ƙarƙashin shirin noman Masara, wanda Alhaji Rufai Muazu Dikko, da aka fi sani da Sarkin Labar, ke sanya ido.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Har ila yau, manoman sun ce; bisa wannan asarar da suka tabka, hakan ya sanya sun gaza mayar da kuɗaɗen da suka kashe, bayan sun yi girbi a kakar noman ta bara.

Suka ƙara da cewa, an faro shirin aikin noman ne, tun a shekarar 2017, wanda aka fara da kadadar noma kimanin  1,000, daga baya kuma aka faɗaɗa shirin zuwa kadada 10,000, inda aka noma kadada dubu 2,143 a Ƙananan Hukumomin Igabi, Soba, Kauru, Zariya da kuma Sabon Gari.

A cewarsu, a ƙarƙashin yarjejeniyar da aka ƙulla, Sarkin Labar ne ya samar da kuɗi da kuma kayan aiki, wanda kuma manoman idan sun yi girbi za su biya da Masara su kuma sayar da sauran abin da suka samu.

Haka zalika, sun bayyana cewa; buhun taki na NPK mai nauyin kilo 50, ana sayar da shi ne a kan kimanin naira 60,000, inda kuma na Urea, farashinsa ya ƙaru zuwa naira 50,000.

Sun ƙara da cewa, wannan dalili ne yasa jimillar kuɗin da suka kashe wajen noman kadada ɗaya ta Masara, kuɗin ya ƙaru zuwa sama da naira miliyan biyu daga naira miiyan ɗaya a bara.  

Manoman sun yi gargaɗin cewa, idan har mahukuntan wannan ƙasa, ba su kawo musu ɗaukin gaggawa ba, ko shakka babu; manoma da dama a Nijeriya, musamman a yankunan Arewa, ba za su iya yin noma a kakar noma ta bana ba.

Kazalika, sun buƙaci babban bankin Nijeriya (CBN), ya samar musu da ɗauki na rage farashin kayan aikin noma da takin zamani, samfurin urea da za su yi amfani da shi a kakar noman ta bana.

A cewarsu, idan babban bankin Nijeriya ya kawo musu ɗauki, su kuma za su biya bankin da wani kaso na Masarar da suka noma, wadda za ta yi daidai da ɗaukin da bankin ya ba su, bayan sun girbe amfanin nasu a kakar ta bana.

Manoman sun kuma bayyana cewa, samar musu da ɗaukin; zai taimaka musu matuƙa wajen sayen amfanin gona a cikin farashi mai rahusa da ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar da kuma ƙara bunƙasa tattalin arziƙin ƙasar, musamman duba da cewa; zaɓukan 2027 na ƙara ƙaratowa nan da ɗan ƙanƙanin lokaci.

Don haka, a cewar tasu; hakan ne kawai zai ba su damar komawa gonakinsu a kakar ta bana, domin ci gaba da noma gonakin nasu.

Kazalika, sun kuma buƙaci son tattaunawa da jami’an gwamnati, domin samun damar tunkarar noman na kakar ta bana.

Noman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Noman

Jiragen Ruwa Guda 32 Ɗauke Da Kaya Sun Sauka A Tashar Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.