Gwamnatin Tarayya ta ce ana amfani da kuɗin da aka samu bayan cire tallafin man fetur wajen ayyukan more rayuwa, farfaɗo da tattalin arziƙi da kuma inganta jin daɗin jama’a.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris ne, ya bayyana hakan ranar Laraba a Abuja yayin wani taron manema labarai tare da Ministan Kuɗi, Taiwo Oyedele, da Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziƙi, Atiku Bagudu.
Idris, ya bayyana cire tallafin man fetur a matsayin ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyen tattalin arziƙi mafi wahala da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta aiwatar.
Ya amince cewa cire tallafin ya jefa mutane, iyalai da ‘yan kasuwa cikin matsaloli, amma ya ce ana mayar da kuɗin da aka samu zuwa ayyukan da za su amfani ’yan Nijeriya.
Ya ce ’yan Nijeriya na da damar sanin adadin kuɗin da aka samu bayan cire tallafin da kuma yadda ake amfani da shi.
Shi ma Ministan Kasafin Kuɗi, Atiku Bagudu, ya ce an ƙaddamar da sauye-sauyen tattalin arziƙin ne domin rage ɓarnar kuɗaɗen gwamnati, ƙara yawan kuɗin shiga da kuma dawo da amincewar masu zuba jari da ’yan Nijeriya.
Ya ce Nijeriya ta daɗe tana fuskantar ƙarancin kuɗin shiga da kuma ƙarancin albarkatun da za a yi amfani da su wajen ci gaba, wanda ya sa sauye-sauyen suka zama dole.
Bagudu ya kuma bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta gaji bashi sama da dala biliyan shida na kuɗaɗen shigo da man fetur, a lokacin da ƙasar ke fama da ƙarancin kuɗi.
Ya ce gwamnati ta ɗauki matakai masu wahala domin daidaita tattalin arziƙin ƙasar, jawo masu zuba jari da kuma samar da ingantattun damar tattalin arziƙi ga ’yan Nijeriya.
Ministan ya yi fatan cewa sauye-sauyen za su inganta harkokin kuɗin gwamnati tare da taimakawa wajen samun ci gaba mai ɗorewa.














