Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, kuma jigo a ADC, Atiku Abubakar, ya ce sauye-sauyen da aka samu a dokokin haraji da takardun da aka sanya hannu a kansu cin amanar ‘yan ƙasa ne, kuma ya saɓa wa kundin tsarin mulki.
Atiku, ya bayyana haka ne a shafukansa na sada zumunta, inda ya ce sauyin ya nuna cewa gwamnati ta fi mayar da hankali kan tara kuɗaɗe daga jama’a fiye da kula da buƙatunsu.
Jigon siyasar ya yi kira da a dakatar da aiwatar da sabbin dokokin harajin da ake sa ran farawa a watan Janairun 2026 domin a gudanar da cikakken bincike.
Ya kuma buƙaci majalisar dokoki ta gyara sauye-sauyen da aka yi ba bisa ƙa’ida ba, a hukunta masu hannu, sannan hukumar EFCC ta gudanar da bincike kan lamarin.















Discussion about this post