Gwamnatin tarayya ta yi gyara ga tuhumar da ake yi wa tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami, da ɗansa Abdulaziz, inda ta cire zargin da ya shafi ɗaukar nauyin ta’addanci.
A zaman kotu na ranar Laraba, lauyan DSS, Akinlolu Kehinde, ya sanar da kotu cewa an yi wa tuhume-tuhumen gyara, tare da neman maye gurbin tsohon tuhume-tuhume da sabon wanda ya fi mayar da hankali kan zargin mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba.
Zaɓen 2027: Malami Zai Fito Takarar Gwamna A Kebbi
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Lauyan waɗanda ake tuhuma, Shaibu Aruwa, ya tabbatar da cewa an ba su sabuwar takardar tuhuma, kuma ba su nuna adawa da karanta ta a gaban kotu ba. Bayan karantawa, Malami da ɗansa sun musanta zargin da ake yi musu.
Alƙaliya Joyce Abdulmalik ta umarci a ci gaba da bin sharuɗɗan belin da aka ba su tun a watan Fabrairu, tare da ɗage shari’ar zuwa ranakun 26 ga Mayu da 15 ga Yuni domin fara sauraron ƙara.
A cikin sabuwar tuhumar, masu gabatar da ƙara sun ce an samu bindigogi da harsasai a gidan Malami da ke Birnin Kebbi, yayin da a baya an tuhume shi da laifuka biyar ciki har da zargin ɗaukar nauyin ta’addanci da kuma mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba.















Discussion about this post