Ministan Albarkatun Ruwa da Tsaftar Muhalli, Joseph Utsev, ya bayyana cewa jihohi 33 da Babban Birnin Tarayya (FCT) za su fuskanci ambaliya a shekarar 2026, inda ake garuruwa 14,118 a matsayin masu fuskantar haɗarin gaske.
Ya bayyana hakan ne a Abuja yayin ƙaddamar da rahoton hasashen ambaliya na shekarar 2026 da Nigeria Hydrological Services Agency ta fitar, yana mai cewa al’ummomin na cikin ƙananan hukumomi 266 bisa nazarin kimiyya da bayanan ruwa.
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Jihohin da abin ya shafa sun haɗa da Kano, Borno, Lagos, Kwara da wasu da dama, yayin da al’ummomi 15,597 a ƙananan hukumomi 405 ke fuskantar matsakaicin haɗari, sai kuma 923 a ƙananan hukumomi 77 da ke cikin ƙananan haɗari.
Ministan ya yi gargaɗin yiwuwar ambaliyar gaggawa a manyan birane kamar Abuja, Lagos da Kano, tare da ambaliyar bakin teku a jihohin kudancin ƙasar sakamakon tashin matakin teku da kuma guguwar ruwa.
A nasa ɓangaren, Bola Ahmed Tinubu ya ce ambaliya na ci gaba da zama babbar barazana ga ƙasa, yana mai kira ga jihohi da su ɗauki matakan kariya, da inganta hanyoyin magudanar ruwa, da kuma shiryawa tun da wuri domin rage asara da kare















Discussion about this post