Gwamnatin tarayya ta kafa sashen tsaron makarantu a cikin ma’aikatar ilimi ta ƙasa a matsayin wani sabon yunkuri na ƙarfafa tsaro ga ɗalibai tare da inganta sha’anin tsaro a makarantu a faɗin Nijeriya
Ministan ilimi Maruf Tunji Alausa ne ya bayyana haka a lokacin da ya halarci gaban kwamitin tsaron na majalisa, wanda ya ce sashen zai ƙarfafa shugabancin manyan makarantu tare da samun daidaiton tsaron su a faɗin Nijeriya
Alausa ya yi bayanin cewa sashen zai maye tsohon sashen kula da tsaron makarantu da ake da shi, wanda kuma zai kasance ya ƙarfafa shugabanci da daidaito tare da lura da makarantu a faɗin Nijeriya
“Ma’aikatar ilimi ta gwamnatin tarayya ta kammala kafa wannan sashe na kula da tsaron makarantu da ƙarfafa shugabanci da samun daidaiton shirin tsaron makarantu a ƙasa baƙi ɗaya” inji minista
Ya kuma yi bayanin cewa ma’aikatar ilimi zata sanya ido akan shirin tsaron makarantu na bai ɗaya tare da aiki akan manhaji iri ɗaya wajen inganta aiwatar da gaskiya da rikon amana tare da sanya ido a dukkanin ƙananan hukumomi 774 na Nijeriya.
A cewar sa, ma’aikatar ilimi haɗin gwiwa da ofishin mai baiwa shugaban ƙasa shawara akan harkokin tsaro da hukumar DSS da Sojoji da Ƴan Sanda da sibil difans tare da sauran hukumomin tsaro za su ƙarfafa harkokin tsaro a zagayen makarantu
Kazalika ministan ya ƙara da cewa kare makarantu ba abu bane da za a tunkara da sanyi jiki ba, yana buƙatar hannun jami’an tsaro da yawa da samar walwala ta yadda za a fuskanci ƙalubalen baƙi ɗaya.
“Hukumomin tsaron mu za su cigaba da ƙoƙari a dokance, sannan ma’aikatar zata samar da doka ta yadda za ariƙa bin abin sau da ƙafa, tare da haɗin gwiwar jihohi domin ganin kowace makaranta ta amfana da shirin” inji shi
Dangane da kuɗaɗen da aka ware domin shirin tsaron makarantu, Alausa ya ce wasu daga cikin tallafin kuɗaɗen da aka amince da su an riga an gama dubawa a halin yanzu, an fitar da su ne kafin a naɗa shi kan muƙaminsa, kuma a wancan lokacin ma’aikatar kuɗi ta tarayya ce ke kula da gudanar da su.












