Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani Kwamitin Haɗin Gwiwa domin nazarin ayyuka, hurumin aiki da tsarin gudanarwa na manyan hukumomin tsaro da na taimakon tsaro, ciki har da Rundunar ‘Yansanda (NPF), DSS, da NSCDC), a wani yunƙuri na sake tsara tsarin tsaron Nijeriya.
An ƙaddamar da kwamitin ne a Abuja ranar Laraba ta hannun Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, wanda ya ce an kirkiro wannan tsari ne domin dakile yawaitar hukumomin tsaro na tarayya, jihohi da kuma masu zaman kansu da ke ƙara yawa a faɗin ƙasar.
Akume, wanda Babban Sakatare na ayyukan bai-ɗaya Dr. Ibrahim Abubakar Kana, ya wakilta, ya ce yawaitar hukumomin tsaro da na taimakon tsaro ya haifar da matsaloli kamar maimaita ayyuka, rikice-rikicen hurumi, da rashin inganci wajen gudanar da aiki.
A cewar wata sanarwa da Shugaban Sashen Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Ofishin SGF, Chris Ugwuegbulam, ya fitar, rahoton kwamitin zai zama jagora ga Gwamnatin Tarayya wajen yanke shawara mai inganci kan yadda za a tsara daidaitaccen tsarin hukumomin tsaro na taimako a ƙasar.
Ya kuma bayyana cewa kwamitin zai tattara cikakken bayani kan dukkan hukumomin tsaro da na taimakon tsaro a matakan tarayya, jihohi da kuma masu zaman kansu.















Discussion about this post