ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin APC Sun Goyi Bayan Tsarin Jam’iyyar Na Aiwatar Da Tazarce A Mukaman Jam’iyyar

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
APC

Kungiyar Gwamnonin Ci Gaba (PGF) na jam’iyyar (APC) ta yanke shawarar ci gaba da rike shugabancin kasa na jam’iyya na yanzu, tare da kin daukar kowanne mataki na sake rabon manyan mukamai.

An cimma wannan shawara da safe a ranar Litinin, bayan taron da ya kare kusan karfe 1:45 na daren ranar a Legas.

  • Idan Ana Fatan Cimma Nasara A Matakin Kasa Da Kasa, Wajibi Ne A Zabi Kasar Sin 
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

Shugaban kungiyar kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, wanda ya yi wa ‘yan jarida bayani bayan taron, ya ce gwamnonin sun amince cewa babu hujja da za ta sa a canza tsarin shugabancin jam’iyya yayin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke kan kujerarsa.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa taron ya kuma duba abubuwan da ke faruwa a Iran da tasirinsu ga tattalin arzikin Nijeriya, musamman a fannin makamashi da hanyoyin samar da kayayyaki na duniya.

A cikin sanarwar da aka fitar a karshen taron, wanda Uzodimma ya sa hannu a kai, kungiyar ta ce ta tattauna kan ci gaban kasa, nauyin shugabancin jihohi, da rawar da gwamnonin ci gaba ke takawa wajen fassara gyare-gyaren gwamnatin tarayya zuwa amfani ga ‘yan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Gwamnonin sun sake tabbatar da jajircewarsu ga daidaiton dimokuradiyya, mulki bisa ka’ida, da Shirin Fatan Sabuntawa na gwamnatin Tinubu.

Sun bayyana cewa kafin taron, ‘yan kungiyar sun ziyarci Shugaba, inda tattaunawa ta ta’allaka kan tsaro, gyare-gyaren tattalin arziki, jin dadin jama’a, ci gaban ababen more rayuwa, tsarin abinci, da karfafa hadin gwiwar tarayya da jihohi.

“Kungiyar ta lura cewa ziyara ta baya-bayan nan da Shugaba ya kai Birtaniya wani bangare ne na babban shirin diflomasiyya na tsaro da ci gaba, kuma ta yi maraba da tabbacin ci gaba da huldar kasa da kasa wajen magance matsalolin tsaro da bunkasa manufofin ci gaba,” in ji sanarwar.

Gwamnonin sun kuma gode wa Shugaba kan “bayyananniyar manufa, gaskiya a cikin shugabanci, da jajircewarsa wajen gina kasa mai karfi.”

Kan batutuwan kasa, kungiyar ta duba yanayin siyasa, tattalin arziki da tsaro, inda ta lura cewa gyare-gyare sau da yawa suna zuwa da kalubale amma suna da muhimmanci don daidaito da ci gaba na dogon lokaci.

Ta jaddada bukatar hadin kai mai karfi tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi, musamman a muhimman sassa kamar noma, makamashi, sufuri, lafiya da ilimi, yayin da ake kiyaye ‘yancin jihohi.

Kan tattalin arziki, kungiyar ta amince da wahalhalun da ke tattare da gyare-gyaren da ake yi amma ta jaddada cewa nasarar su ya kamata a auna ta ingancin rayuwar ‘yan Nijeriya.

Ta gargadi cewa rikicin da ke ci gaba a yankin Gulf na iya kara hauhawar farashi da tsadar kayan aiki, tare da kira ga hadin gwiwa don kara samar da abinci, tallafa wa kananan ‘yan kasuwa da fadada shirye-shiryen jin dadin jama’a.

Gwamnonin sun kuma sake jaddada cewa tsaro shi ne ginshiki ga ci gaban kasa, tare da kiran a ci gaba da saka hannun jari a fannin leken asiri, fasaha, kula da iyakoki da tsarin gargadin gaggawa a matakin al’umma.

APC
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
APC
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Matsin Tattalin Arziki: Wani Magidanci Ya Rataye Kansa A Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
APC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
APC

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
APC

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.