ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Yaba Da Ci Gaban Da Tinubu Ya Samar A Yankin

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
gombe

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce; sauye-sauyen da Shugaba Bola Tinubu ya yi, na iya zama kalubale, amma suna kan kafa wani harsashin na ci gaba.

Da yake jaddada goyon bayan taron ga Tinubu, Inuwa ya yaba wa shugaban kasa kan jagorancinsa na kawo sauyi, yayin da ya cika shekara 74.

  • Shettima Ya Nemi Hadin Kan Kafafen Yada Labaru Domin Samar Da Ci Gaba
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata A Rikicin ‘Yan Daba A Kano

A cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai na gidan gwamnatin Gombe, Ismaila Uba Misilli ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, gwamnan, wanda yake magana a madadin takwarorinsa, ya bayyana jagorancin shugaba Tinubu a matsayin jajirtacce da kuma jigon tabbatar da dorewar kwanciyar hankali da sauye-sauyen tattalin arzikin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Gwamna Inuwa, ya bayyana cewa; tun bayan hawansa karagar mulki, shugaban ya nuna jajircewa wajen aiwatar da sauye-sauye masu ma’ana da nufin sake farfado da tattalin arzikin kasa da kuma karfafa muhimman cibiyoyi.

Haka zalika, ya amince da cewa; duk da cewa sauye-sauyen sun zo da wasu kalubale da sadaukarwa, amma matakai ne masu muhimmanci na gina kyakkyawar makoma mai dorewa da wadata ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A cewarsa, shirin ‘Renewed Hope Agenda’ na shugaban kasar, ya ci gaba da sake farfado da amincewa a tsakanin ‘yan kasa tare da kafa wata hanya mai kyau, don ci gaba mai dorewa da samun cikakken hadin kai na kasa.

Shugaban ya kuma jaddada cewa, Jihar Gombe tare da hadin gwiwar sauran Jihohin Arewa, sun ci gaba da jajircewa wajen ganin an samu nasarar aiwatar da manufofi da shirye-shiryen shugaban kasa.

“Sauye-sauyen da shugaban kasa ya dauka na kawo ci gaba, na nuni da jagorancin da ke tattare da yakini da kuma burin tabbatar da kyakkyawar makoma ga al’ummar kasar. Koda-yake akwai kalubale, wadannan sauye-sauyen sun riga sun kafa tushen ci gaba mai dorewa,” in ji shi.

Kazalika, ya kuma kara jaddada goyon bayan hadin gwiwar gwamnonin Arewa, don ci gaba da aiwatar da ajandar kawo sauyi ga shugaban kasa fiye da yadda ake gudanar da mulki a halin yanzu.

“Mu a Jihar Gombe tare da takwarorinmu na kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, muna godiya da goyon bayan da kuke bai wa gwamnatocin kananan hukumomi da tsarin tafiyar da harkokin mulki na kasa baki-daya, mun tsaya tsayin daka tare da ku, muna kara jaddada goyon bayanmu ga shugabancinku da hangen nesa yanzu da kuma nan gaba.

Gwamna Inuwa, ya kuma yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya da nisan kwana.

Arewa
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sin Za Ta Sanya Fa’idojin Tattara Bayanai Su Amfanar Da Jama’ar Duk Duniya

Sin Za Ta Sanya Fa’idojin Tattara Bayanai Su Amfanar Da Jama’ar Duk Duniya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.