ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Yaba Da Ci Gaban Da Tinubu Ya Samar A Yankin

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
gombe

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce; sauye-sauyen da Shugaba Bola Tinubu ya yi, na iya zama kalubale, amma suna kan kafa wani harsashin na ci gaba.

Da yake jaddada goyon bayan taron ga Tinubu, Inuwa ya yaba wa shugaban kasa kan jagorancinsa na kawo sauyi, yayin da ya cika shekara 74.

  • Shettima Ya Nemi Hadin Kan Kafafen Yada Labaru Domin Samar Da Ci Gaba
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata A Rikicin ‘Yan Daba A Kano

A cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai na gidan gwamnatin Gombe, Ismaila Uba Misilli ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, gwamnan, wanda yake magana a madadin takwarorinsa, ya bayyana jagorancin shugaba Tinubu a matsayin jajirtacce da kuma jigon tabbatar da dorewar kwanciyar hankali da sauye-sauyen tattalin arzikin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Gwamna Inuwa, ya bayyana cewa; tun bayan hawansa karagar mulki, shugaban ya nuna jajircewa wajen aiwatar da sauye-sauye masu ma’ana da nufin sake farfado da tattalin arzikin kasa da kuma karfafa muhimman cibiyoyi.

Haka zalika, ya amince da cewa; duk da cewa sauye-sauyen sun zo da wasu kalubale da sadaukarwa, amma matakai ne masu muhimmanci na gina kyakkyawar makoma mai dorewa da wadata ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A cewarsa, shirin ‘Renewed Hope Agenda’ na shugaban kasar, ya ci gaba da sake farfado da amincewa a tsakanin ‘yan kasa tare da kafa wata hanya mai kyau, don ci gaba mai dorewa da samun cikakken hadin kai na kasa.

Shugaban ya kuma jaddada cewa, Jihar Gombe tare da hadin gwiwar sauran Jihohin Arewa, sun ci gaba da jajircewa wajen ganin an samu nasarar aiwatar da manufofi da shirye-shiryen shugaban kasa.

“Sauye-sauyen da shugaban kasa ya dauka na kawo ci gaba, na nuni da jagorancin da ke tattare da yakini da kuma burin tabbatar da kyakkyawar makoma ga al’ummar kasar. Koda-yake akwai kalubale, wadannan sauye-sauyen sun riga sun kafa tushen ci gaba mai dorewa,” in ji shi.

Kazalika, ya kuma kara jaddada goyon bayan hadin gwiwar gwamnonin Arewa, don ci gaba da aiwatar da ajandar kawo sauyi ga shugaban kasa fiye da yadda ake gudanar da mulki a halin yanzu.

“Mu a Jihar Gombe tare da takwarorinmu na kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, muna godiya da goyon bayan da kuke bai wa gwamnatocin kananan hukumomi da tsarin tafiyar da harkokin mulki na kasa baki-daya, mun tsaya tsayin daka tare da ku, muna kara jaddada goyon bayanmu ga shugabancinku da hangen nesa yanzu da kuma nan gaba.

Gwamna Inuwa, ya kuma yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya da nisan kwana.

Arewa
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Sin Za Ta Sanya Fa’idojin Tattara Bayanai Su Amfanar Da Jama’ar Duk Duniya

Sin Za Ta Sanya Fa’idojin Tattara Bayanai Su Amfanar Da Jama’ar Duk Duniya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.