ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Yaba Da Ci Gaban Da Tinubu Ya Samar A Yankin

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
gombe

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce; sauye-sauyen da Shugaba Bola Tinubu ya yi, na iya zama kalubale, amma suna kan kafa wani harsashin na ci gaba.

Da yake jaddada goyon bayan taron ga Tinubu, Inuwa ya yaba wa shugaban kasa kan jagorancinsa na kawo sauyi, yayin da ya cika shekara 74.

  • Shettima Ya Nemi Hadin Kan Kafafen Yada Labaru Domin Samar Da Ci Gaba
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata A Rikicin ‘Yan Daba A Kano

A cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai na gidan gwamnatin Gombe, Ismaila Uba Misilli ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, gwamnan, wanda yake magana a madadin takwarorinsa, ya bayyana jagorancin shugaba Tinubu a matsayin jajirtacce da kuma jigon tabbatar da dorewar kwanciyar hankali da sauye-sauyen tattalin arzikin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Gwamna Inuwa, ya bayyana cewa; tun bayan hawansa karagar mulki, shugaban ya nuna jajircewa wajen aiwatar da sauye-sauye masu ma’ana da nufin sake farfado da tattalin arzikin kasa da kuma karfafa muhimman cibiyoyi.

Haka zalika, ya amince da cewa; duk da cewa sauye-sauyen sun zo da wasu kalubale da sadaukarwa, amma matakai ne masu muhimmanci na gina kyakkyawar makoma mai dorewa da wadata ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

A cewarsa, shirin ‘Renewed Hope Agenda’ na shugaban kasar, ya ci gaba da sake farfado da amincewa a tsakanin ‘yan kasa tare da kafa wata hanya mai kyau, don ci gaba mai dorewa da samun cikakken hadin kai na kasa.

Shugaban ya kuma jaddada cewa, Jihar Gombe tare da hadin gwiwar sauran Jihohin Arewa, sun ci gaba da jajircewa wajen ganin an samu nasarar aiwatar da manufofi da shirye-shiryen shugaban kasa.

“Sauye-sauyen da shugaban kasa ya dauka na kawo ci gaba, na nuni da jagorancin da ke tattare da yakini da kuma burin tabbatar da kyakkyawar makoma ga al’ummar kasar. Koda-yake akwai kalubale, wadannan sauye-sauyen sun riga sun kafa tushen ci gaba mai dorewa,” in ji shi.

Kazalika, ya kuma kara jaddada goyon bayan hadin gwiwar gwamnonin Arewa, don ci gaba da aiwatar da ajandar kawo sauyi ga shugaban kasa fiye da yadda ake gudanar da mulki a halin yanzu.

“Mu a Jihar Gombe tare da takwarorinmu na kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, muna godiya da goyon bayan da kuke bai wa gwamnatocin kananan hukumomi da tsarin tafiyar da harkokin mulki na kasa baki-daya, mun tsaya tsayin daka tare da ku, muna kara jaddada goyon bayanmu ga shugabancinku da hangen nesa yanzu da kuma nan gaba.

Gwamna Inuwa, ya kuma yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya da nisan kwana.

Arewa
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Sin Za Ta Sanya Fa’idojin Tattara Bayanai Su Amfanar Da Jama’ar Duk Duniya

Sin Za Ta Sanya Fa’idojin Tattara Bayanai Su Amfanar Da Jama’ar Duk Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.