ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shettima Ya Nemi Hadin Kan Kafafen Yada Labaru Domin Samar Da Ci Gaba

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
Shettima

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya nemi hadin kan kafafen yada labaran Nijeriya domin samar da ci gaba tare da gwamnatin tarayya ta hanyar amfani da manhajojinsu wajen karfafa dimokuradiyyar kasa ta hanyar aikin jarida mai amfani da tunani mai zurfi.

Ya ce al’umma ba ta lalacewa saboda rashin ra’ayoyi, amma saboda rashin maza da mata masu kwarin gwiwa don bincikan ra’ayoyi da gwada su da hankali da kuma tambayoyi masu wuya wadanda ke ceto mutane daga bin ra’ayoyinsu na hankali.

  • Ba Za A Iya Daidaita Batun Mashigin Hormuz Ba Har Sai An Kawo Karshen Yaki
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da ‘Yan Nijeriya 1,231 Daga Jamhuriyar Nijar A Mako Daya

A cewar wata sanarwa daga mai magana da yawun mataimakin shugaban kasa, Stanley Nkwocha, Sanata Shettima ya yi jawabi a jiya a Abuja yayin kaddamar da wani littafi da bikin shekaru 60 na haihuwar kwararren dan jarida, Mista Babajide Kolade-Otitoju.

ADVERTISEMENT

Ya yaba wa gudunmawar Babajide ga aikin jarida da tunanin mai zurfi, yana mai cewa shirin talabijin dinsa da aka fi sani da “Journalists Hangout,” ya samu damar habaka bincike a Nijeriya.

Dangane da rawar da kafofin watsa labarai ke takawa wajen karfafa dimokuradiyya, mataimakin shugaban kasa ya ce, “Ma’aunin kowace dimokuradiyya shi ne, ba wai gudanar da zabe ba ne kawai, akwai wayar da kan da jan hankai na kafofin watsa labarai. Dimokuradiyya na dogara ne ga kafofin watsa labarai da ke sanin lokacin tambayoyi, lokacin gargadi, lokacin bayar da misalai da lokacin kauce wa rikice-rikice abokan hulda.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Komai yana lalacewa ne idan ba a yin tambayoyi a kansa. Matsayi yana lalacewa. Hukumomi na lalacewa. Tattaunawar kasa tana lalacewa. Ko gaskiya da kanta na iya yin shiru idan aka bar karya tare da kalubalantarta ba. Kafofin watsa labarai ba wurin hayaniya ba ne. Sun kasance wajen fadakar da al’umma.”

Mataimakin shugaban kasa Shettima ya yi wa Babajide yabo mai girma a ranar haihuwarsa ta shekara 60, yana bayyana shi a matsayin mutum wanda ya mayar da bincikan abubuwan da suke amfanan rayuwar al’umma domin su samu mafita daga abubuwan da suka shige musu duhu.

Ya ce Babajide cikakken misali na irin wadannan maza da mata da ya kamata a samu, har ma da bayyana shi a matsayin mai inganta dimokuradiyya wanda ya cancanci a yi bikin zagayowar haihuwarsa.

“A yau, yayin da muke bikin zagayowar ranar haihuwarka ta shekara 60 da gabatar da littafinka, muna girmama abubuwan da ka gabatar a cikin wadancan shekarun.

“Muna girmama sana’ar da kuka daraja, wata kafa da kuka daga darajarta, da tattaunawa mai zurfi da kuka taimaka wajen raya ta a kasarmu. Haka kuma muna girmama shawararku ta rubutu, don tuna abubuwa, da barin wani tarihi na rayuwa da aka sadaukar don tunani,”.

Ya kara yabawa Kolade-Otitoju saboda sadaukar da rayuwarsa ga aiki mai wahala domin al’umma su amfana. Ya jaddada cewa ba karamin aiki ba ne yin aiki a matsayin dan jarida tsawon shekaru tare da kare mutuncinsa har yanzu.

“Wannan ba karamin nasara ba ce. Yin shekaru da dama a aikin jarida tare da kiyaye gaskiya ba karamin namijin kokari ya yi ba, kuma har yanzu yana nan a kan turbarsa ta asali, wata gagarumar nasara ce,” ya kara da cewa.

A nasa bangaren, shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya kuma Gwamnan Jihar Kwara, Alhaji Abdulrahman AbdulRazak, yayin da yake yaba halayen wanda ake taya shi murnar zagayowar shakarar haihuwa, ya yi kirari da kafafen yada labarai saboda gudummawar da suke bai wa dimokuradiyya da ci gaban Nijeriya.

A nasa bangaren, Farfesa Kyari Mohammed, ya ce littafin mai babi tara yana dauke da aikin kwarewar Babajide-Otitoju da aikinsa a matsayin dan jarida da ya yi fice a duniyar wajen buguwa da watsa shirye-shirye, yana nuna zurfin kwarewarsa da tasirin gudummawarsa ga ilimi da aikin jarida a Nijeriya da ma duniya baki daya.

Ya ce littafin yana bayar da labari ne na musamman game da ra’ayin marubucin kan siyasa da mulki, aikin jarida kuma ya ba da shawara ga masu tsara manufofi, ‘yan jarida masu aiki da kuma masu gudanarwa a bangarorin gwamnati da na masu zaman kansu.

Tun da farko a jawabinsa, tsohon daraktan janar na hukumar kula da kafofin yada labarai ta kasa (NBC), Malam Danladi Bako, ya yaba wa halayen Mista Babajide-Otitoju, yana bayyana shi a matsayin jarumi.

Ya gode tare da yaba wa mataimakin shugaban kasa saboda girmama mai bikin da daukacin ‘yan jarida da aikin jarida.

A cikin wasu bayanai daban-daban, mai magana da yawun shugaban kasa, Mista Sunday Dare da mai gabatar da shirin AIT, Mista Gbenga Aruleba, da shugaban hukumar kula da ‘yan Nijeriya a kasashen waje (NiDCOM), Hon. Abike Dabiri, wanda ya yi jawabi a madadin tsoffin abokan aiki na wanda ake murnar ranar haihuwarsa, sun yi masa yabo da kuma godiya ga gudunmawarsa ga aikin jarida da ci gaban dimokuradiyya a Nijeriya.

Haka kuma a wurin taron akwai jagoran majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele da Gwamnonin Umo Eno na Akwa Ibom da Babajide Sanwo-Olu na Legas da Kefas Agbu na Taraba da Usman Ahmed Ododo na Kogi da Babagana Zulum na Borno da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila, mashawarci na musamman ga shugaban kasa kan yada labarai, Mista Bayo Onanuga, da tsohon babban lauyan tarayya, Malam Mohammed Adoke, da sauran su.

Shettima
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Shettima
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Tsaurara Matakan Fatattakar Haramtattun Harkoki A Sashen Kudi

Sin Ta Tsaurara Matakan Fatattakar Haramtattun Harkoki A Sashen Kudi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.