ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Yi Tir Da Tashin Bama-bamai A Maiduguri

by Khalid Idris Doya
3 months ago
Arewa

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allawadai da fashewar jerin bama-bamai masu muni da suka girgiza Maiduguri a ranar Litinin, inda ya bayyana harin a matsayin na rashin imani, na ta’addanci a kan fararen hula.

Rahotanni sun nuna cewa tashin jerin bama-bamai wadanda wasu ‘yan kunar bakin wake suka aiwatar sun tashi ne a lokaci guda da yammacin ranar Litinin a kasuwar Maiduguri Monday Market, kofar shiga asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH) da kuma Post- Office flyober dukka a Maiduguri babbar birnin jihar Borno.

  • Shettima Ya Ziyarci Waɗanda Harin Bam Ya Shafa A Maiduguri
  • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin

‘Yansanda sun ce mutane 23 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu sama da 100 suka jikkata.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar da ya fitar a matsayinsa na Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matukar jimami da alhininsa kan wannan mummunan hare-haren, tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno, musamman iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu.

Inuwa wanda kuma shi ne gwamnan jihar Gombe ya ce, “Wannan mummunan aika-aikar na tashin hankali ba wai kawai abin kyama ba ne, wani yunkuri ne na zalunci da nufin haifar da tsoro da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar da ake kokarin dawo da shi a yankin Arewa maso Gabas.”

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sanarwar da Isma’ila Uba Misilli, Darakta-Janar na harkokin yada labarai na gidan jihar gwamnatin Gombe ya sanya wa hannu, Gwamna Inuwa ya ce, dole ne a yi Allah-wadai da hare-haren.

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa ya jajanta wa wadanda ke kwance a asibiti a halin yanzu domin samun kulawar likitoci sakamakon raunuka da suka samu a hare-haren, tare da yi musu addu’ar samun sauki cikin gaggawa.

Kazalika, ya kuma yaba wa jami’an agajin gaggawa da hukumomin tsaro kan yadda suka gaggauta daukar mataki wajen shawo kan halin da aka shiga bayan fashe-fashen.

Ya sake jaddada kudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da aiki kafada-kafada da Gwamnatin Tarayya da kuma hukumomin tsaro domin yakar dukkan nau’o’in ta’addanci da ayyukan laifi da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar arewa maso gabas.

Inuwa ya budaci mazauna al’ummar Maiduguri da sauran yankunan da suke shiyyar da su kwantar da hankulansu, su kasance masu ci gaba da bin doka da oda, tare da bada cikakken hadin kai da hukumomin tsaro ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen binciken da ake yi da kuma taimaka musu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso domin dakile ayyukan ta’addanci.

“A halin yanzu fiye da kowane lokaci, wajibi ne mu tsaya tsayin daka tare domin yakar makiyan zaman lafiya. Ba za mu yi kasa a guiwa kan yunkurinmu na dawo da zaman lafiya a shiryar arewa maso gabas ba, tare za mu kawo karshen wannan matsalar tsaron,” ya jaddada.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu a wannan hare-haren, tare da kira ga hukumomin tsaron da su kara zage damtse domin ganin an kamo wadanda suka aikata wannan mummunan aika-aikar kuma a hukunta su cikin gaggawa.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: Matakin Amurka Na Kaddamar Da Yaki Zai Rage Karfinta Na Babakere

Nazarin CGTN: Matakin Amurka Na Kaddamar Da Yaki Zai Rage Karfinta Na Babakere

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.