ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Yi Tir Da Tashin Bama-bamai A Maiduguri

by Khalid Idris Doya
3 months ago
Arewa

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allawadai da fashewar jerin bama-bamai masu muni da suka girgiza Maiduguri a ranar Litinin, inda ya bayyana harin a matsayin na rashin imani, na ta’addanci a kan fararen hula.

Rahotanni sun nuna cewa tashin jerin bama-bamai wadanda wasu ‘yan kunar bakin wake suka aiwatar sun tashi ne a lokaci guda da yammacin ranar Litinin a kasuwar Maiduguri Monday Market, kofar shiga asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH) da kuma Post- Office flyober dukka a Maiduguri babbar birnin jihar Borno.

  • Shettima Ya Ziyarci Waɗanda Harin Bam Ya Shafa A Maiduguri
  • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin

‘Yansanda sun ce mutane 23 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu sama da 100 suka jikkata.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar da ya fitar a matsayinsa na Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matukar jimami da alhininsa kan wannan mummunan hare-haren, tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno, musamman iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu.

Inuwa wanda kuma shi ne gwamnan jihar Gombe ya ce, “Wannan mummunan aika-aikar na tashin hankali ba wai kawai abin kyama ba ne, wani yunkuri ne na zalunci da nufin haifar da tsoro da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar da ake kokarin dawo da shi a yankin Arewa maso Gabas.”

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sanarwar da Isma’ila Uba Misilli, Darakta-Janar na harkokin yada labarai na gidan jihar gwamnatin Gombe ya sanya wa hannu, Gwamna Inuwa ya ce, dole ne a yi Allah-wadai da hare-haren.

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa ya jajanta wa wadanda ke kwance a asibiti a halin yanzu domin samun kulawar likitoci sakamakon raunuka da suka samu a hare-haren, tare da yi musu addu’ar samun sauki cikin gaggawa.

Kazalika, ya kuma yaba wa jami’an agajin gaggawa da hukumomin tsaro kan yadda suka gaggauta daukar mataki wajen shawo kan halin da aka shiga bayan fashe-fashen.

Ya sake jaddada kudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da aiki kafada-kafada da Gwamnatin Tarayya da kuma hukumomin tsaro domin yakar dukkan nau’o’in ta’addanci da ayyukan laifi da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar arewa maso gabas.

Inuwa ya budaci mazauna al’ummar Maiduguri da sauran yankunan da suke shiyyar da su kwantar da hankulansu, su kasance masu ci gaba da bin doka da oda, tare da bada cikakken hadin kai da hukumomin tsaro ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen binciken da ake yi da kuma taimaka musu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso domin dakile ayyukan ta’addanci.

“A halin yanzu fiye da kowane lokaci, wajibi ne mu tsaya tsayin daka tare domin yakar makiyan zaman lafiya. Ba za mu yi kasa a guiwa kan yunkurinmu na dawo da zaman lafiya a shiryar arewa maso gabas ba, tare za mu kawo karshen wannan matsalar tsaron,” ya jaddada.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu a wannan hare-haren, tare da kira ga hukumomin tsaron da su kara zage damtse domin ganin an kamo wadanda suka aikata wannan mummunan aika-aikar kuma a hukunta su cikin gaggawa.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: Matakin Amurka Na Kaddamar Da Yaki Zai Rage Karfinta Na Babakere

Nazarin CGTN: Matakin Amurka Na Kaddamar Da Yaki Zai Rage Karfinta Na Babakere

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.