ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Jihohin Kudu Maso Yammacin Nijeriya Sun Jaddada Bukatar Kafa ‘Yansandan Jihohi

by Sani Anwar and Sulaiman
8 months ago
Gwamnoni

Kungiyar Gwamnonin Kudu-maso-yamma, ta yi kira da a kafa ‘yansandan jihohi, biyo bayan karuwar rashin tsaro a fadin kasar nan.

Gwamnonin sun kuma ja hankalin gwamnatin tarayya, kan abin da ta kira bukatar inganta yanayin dazuzzuka a fadin jihohin yankunan.

  • PRP Ta Gargadi Sabon Shugaban PDP Kan Neman Taimakon Kasashen Waje A Rikicin Jam’iyya
  • Tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai, Ya Fice Daga SDP, Ya Koma ADC

Taron ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar ta yi wani abu a kan dimbin dazuzzukan da ta ce, sun zama maboyar ‘yan ta’adda.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar, bayan wani taro da suka yi a birnin Ibadan na jihar Oyo, dukkanin gwamnonin shida; sun amince da cewa, gwamnatin tarayya ta taimaka; musamman wajen tura jami’an tsaro na gandun daji zuwa fadin jihohin Kudu-maso-yamma, inda kowace gwamnatin jihar ke da alhakin samar da ma’aikatan da ake bukata.

Shugaban kungiyar, kuma Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ne ya karanta jawabin taron.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kazalika, wadanda suka halarci taron; sun hada da Gwamnoni Dapo Abiodun na Ogun; Biodun Oyebanji na Ekiti; Lucky Aiyedatiwa na Ondo; Ademola Adeleke na Osun, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi; da gwamnan mai masaukin baki, Seyi Makinde.

A cikin sanarwar, taron ya amince da kafa asusun tsaro na Kudu-maso-yamma (SWSF), a karkashin Hukumar DAWN, wanda kungiyar masu ba da shawara ta musamman kan harkokin tsaro, na dukkanin jihohin Kudu-maso-yamma, za ta gudanar tare da yin taro a kowane wata.

Domin inganta tattara bayanan sirri da kuma saurin mayar da martani a cikin jihohi shida, dandalin ya dauki hanyar sadarwar ta zamani (dijital) guda daya.

“Zauren ya kudiri aniyar kafa tsarin raba bayanan sirri kai tsaye a tsakanin dukkanin jihohin Kudu-maso-yamma guda shida (Legas, Ogun, Oyo, Osun, Ondo da Ekiti), wannan dandali zai yi musayar sanarwar barazana, taswirar abubuwan da suka faru, sanarwar matafiya da kaya tare da daidaita matakin gaggawa daga jiha zuwa jiha.”

Sanarwar ta kuma nuna damuwa a kan kutsawa dazuzzukan da gungun masu aikata laifuka ke yi, inda ta bukaci taimakon gwamnatin tarayya, wajen tura jami’an gandun dazuzzukan tare da jaddada aniyar gwamnonin na tabbatar da kare dazuzzukan.

Da yake magana a kan matsalar kaura zuwa yankin Kudu-maso-yamma ba tare da ka’ida ba, taron ya jaddada bukatar tsaurara matakan kula da iyakoki da inganta tsarin tantancewa.

“Kungiyar ta kuma nuna matukar damuwa game da yin kaurar, ba bisa ka’ida ba da ke ci gaba da haifar da kalubale a fadin yankin na Kudu-maso- yamma.

Ta kara da cewa, “Zauren ya amince da kara karfafa hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da cewa; tafiye-tafiye tsakanin jihohi, ba zai zama wata hanya ta rashin tsaro ba.”

Gwamnoni
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Gwamnoni
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Ranchers Bees Za Su Ci Gaba Da Bugin Wasannin Gida A Filin Bako Kontagora

Ranchers Bees Za Su Ci Gaba Da Bugin Wasannin Gida A Filin Bako Kontagora

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.