ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Jihohin Kudu Maso Yammacin Nijeriya Sun Jaddada Bukatar Kafa ‘Yansandan Jihohi

by Sani Anwar and Sulaiman
6 months ago
Gwamnoni

Kungiyar Gwamnonin Kudu-maso-yamma, ta yi kira da a kafa ‘yansandan jihohi, biyo bayan karuwar rashin tsaro a fadin kasar nan.

Gwamnonin sun kuma ja hankalin gwamnatin tarayya, kan abin da ta kira bukatar inganta yanayin dazuzzuka a fadin jihohin yankunan.

  • PRP Ta Gargadi Sabon Shugaban PDP Kan Neman Taimakon Kasashen Waje A Rikicin Jam’iyya
  • Tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai, Ya Fice Daga SDP, Ya Koma ADC

Taron ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar ta yi wani abu a kan dimbin dazuzzukan da ta ce, sun zama maboyar ‘yan ta’adda.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar, bayan wani taro da suka yi a birnin Ibadan na jihar Oyo, dukkanin gwamnonin shida; sun amince da cewa, gwamnatin tarayya ta taimaka; musamman wajen tura jami’an tsaro na gandun daji zuwa fadin jihohin Kudu-maso-yamma, inda kowace gwamnatin jihar ke da alhakin samar da ma’aikatan da ake bukata.

Shugaban kungiyar, kuma Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ne ya karanta jawabin taron.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Kazalika, wadanda suka halarci taron; sun hada da Gwamnoni Dapo Abiodun na Ogun; Biodun Oyebanji na Ekiti; Lucky Aiyedatiwa na Ondo; Ademola Adeleke na Osun, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi; da gwamnan mai masaukin baki, Seyi Makinde.

A cikin sanarwar, taron ya amince da kafa asusun tsaro na Kudu-maso-yamma (SWSF), a karkashin Hukumar DAWN, wanda kungiyar masu ba da shawara ta musamman kan harkokin tsaro, na dukkanin jihohin Kudu-maso-yamma, za ta gudanar tare da yin taro a kowane wata.

Domin inganta tattara bayanan sirri da kuma saurin mayar da martani a cikin jihohi shida, dandalin ya dauki hanyar sadarwar ta zamani (dijital) guda daya.

“Zauren ya kudiri aniyar kafa tsarin raba bayanan sirri kai tsaye a tsakanin dukkanin jihohin Kudu-maso-yamma guda shida (Legas, Ogun, Oyo, Osun, Ondo da Ekiti), wannan dandali zai yi musayar sanarwar barazana, taswirar abubuwan da suka faru, sanarwar matafiya da kaya tare da daidaita matakin gaggawa daga jiha zuwa jiha.”

Sanarwar ta kuma nuna damuwa a kan kutsawa dazuzzukan da gungun masu aikata laifuka ke yi, inda ta bukaci taimakon gwamnatin tarayya, wajen tura jami’an gandun dazuzzukan tare da jaddada aniyar gwamnonin na tabbatar da kare dazuzzukan.

Da yake magana a kan matsalar kaura zuwa yankin Kudu-maso-yamma ba tare da ka’ida ba, taron ya jaddada bukatar tsaurara matakan kula da iyakoki da inganta tsarin tantancewa.

“Kungiyar ta kuma nuna matukar damuwa game da yin kaurar, ba bisa ka’ida ba da ke ci gaba da haifar da kalubale a fadin yankin na Kudu-maso- yamma.

Ta kara da cewa, “Zauren ya amince da kara karfafa hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da cewa; tafiye-tafiye tsakanin jihohi, ba zai zama wata hanya ta rashin tsaro ba.”

Gwamnoni
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
Gwamnoni
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Ranchers Bees Za Su Ci Gaba Da Bugin Wasannin Gida A Filin Bako Kontagora

Ranchers Bees Za Su Ci Gaba Da Bugin Wasannin Gida A Filin Bako Kontagora

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.