ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Jihohin Kudu Maso Yammacin Nijeriya Sun Jaddada Bukatar Kafa ‘Yansandan Jihohi

by Sani Anwar and Sulaiman
10 months ago
Gwamnoni

Kungiyar Gwamnonin Kudu-maso-yamma, ta yi kira da a kafa ‘yansandan jihohi, biyo bayan karuwar rashin tsaro a fadin kasar nan.

Gwamnonin sun kuma ja hankalin gwamnatin tarayya, kan abin da ta kira bukatar inganta yanayin dazuzzuka a fadin jihohin yankunan.

  • PRP Ta Gargadi Sabon Shugaban PDP Kan Neman Taimakon Kasashen Waje A Rikicin Jam’iyya
  • Tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai, Ya Fice Daga SDP, Ya Koma ADC

Taron ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar ta yi wani abu a kan dimbin dazuzzukan da ta ce, sun zama maboyar ‘yan ta’adda.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar, bayan wani taro da suka yi a birnin Ibadan na jihar Oyo, dukkanin gwamnonin shida; sun amince da cewa, gwamnatin tarayya ta taimaka; musamman wajen tura jami’an tsaro na gandun daji zuwa fadin jihohin Kudu-maso-yamma, inda kowace gwamnatin jihar ke da alhakin samar da ma’aikatan da ake bukata.

Shugaban kungiyar, kuma Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ne ya karanta jawabin taron.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Kazalika, wadanda suka halarci taron; sun hada da Gwamnoni Dapo Abiodun na Ogun; Biodun Oyebanji na Ekiti; Lucky Aiyedatiwa na Ondo; Ademola Adeleke na Osun, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi; da gwamnan mai masaukin baki, Seyi Makinde.

A cikin sanarwar, taron ya amince da kafa asusun tsaro na Kudu-maso-yamma (SWSF), a karkashin Hukumar DAWN, wanda kungiyar masu ba da shawara ta musamman kan harkokin tsaro, na dukkanin jihohin Kudu-maso-yamma, za ta gudanar tare da yin taro a kowane wata.

Domin inganta tattara bayanan sirri da kuma saurin mayar da martani a cikin jihohi shida, dandalin ya dauki hanyar sadarwar ta zamani (dijital) guda daya.

“Zauren ya kudiri aniyar kafa tsarin raba bayanan sirri kai tsaye a tsakanin dukkanin jihohin Kudu-maso-yamma guda shida (Legas, Ogun, Oyo, Osun, Ondo da Ekiti), wannan dandali zai yi musayar sanarwar barazana, taswirar abubuwan da suka faru, sanarwar matafiya da kaya tare da daidaita matakin gaggawa daga jiha zuwa jiha.”

Sanarwar ta kuma nuna damuwa a kan kutsawa dazuzzukan da gungun masu aikata laifuka ke yi, inda ta bukaci taimakon gwamnatin tarayya, wajen tura jami’an gandun dazuzzukan tare da jaddada aniyar gwamnonin na tabbatar da kare dazuzzukan.

Da yake magana a kan matsalar kaura zuwa yankin Kudu-maso-yamma ba tare da ka’ida ba, taron ya jaddada bukatar tsaurara matakan kula da iyakoki da inganta tsarin tantancewa.

“Kungiyar ta kuma nuna matukar damuwa game da yin kaurar, ba bisa ka’ida ba da ke ci gaba da haifar da kalubale a fadin yankin na Kudu-maso- yamma.

Ta kara da cewa, “Zauren ya amince da kara karfafa hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da cewa; tafiye-tafiye tsakanin jihohi, ba zai zama wata hanya ta rashin tsaro ba.”

Gwamnoni
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Gwamnoni
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

MASU ALAKA

Gwamnoni
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwamnoni
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Ranchers Bees Za Su Ci Gaba Da Bugin Wasannin Gida A Filin Bako Kontagora

Ranchers Bees Za Su Ci Gaba Da Bugin Wasannin Gida A Filin Bako Kontagora

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Gwamnoni

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwamnoni

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.