Babban daraktan kungiyar manoman hatsi da sarrafa mai daga albarkatun gona a Afirka ta Kudu Andre van der Vyver ya ce, bunkasar hadin gwiwar noma tare da Sin, na samar da sabbin damarmaki ga manoman Afirka ta Kudu, kuma hakan na kara shigar da sabon kuzari ga hada-hadar sarrafa hajoji, da bunkasar tattalin arzikin yankunan karkarar kasar.
Mista van der Vyver, wanda ya bayyana hakan yayin tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, ya ce hadin gwiwar sassan biyu na da matukar muhimmanci, kuma karkashin hakan, fitar da hajoji zai ingiza sarrafa abubuwa, da kara habaka kimar tattalin arzikin cikin gida, musamman a matakin shiyyar da tattalin arzikin karkara.
Van der Vyver ya kara da cewa, a matsayinta na babbar mai sayen waken soya, kasar Sin na samarwa ‘yan kasuwar Afirka ta Kudu babbar dama, da kasuwa mai fadi, wanda hakan zai bunkasa kasuwa, da tabbaci da ake bukata don tallafawa fadadar sashen noma na Afika ta Kudu.
Kazalika, jami’in ya jinjinawa manufar janye daukacin harajin fito da Sin ta fara aiwatarwa kan hajojin Afirka ta Kudu da suka cika sharudda. A cewarsa, hakan da ma fifikon kasar a fannin shige da ficen hajojin kasuwanci tsakanin abokan takara, sun ci gaba da taka rawar gani wajen tallafawa masu hada-hadar fitar da kaya zuwa ketare. (Saminu Alhassan)














