Ranar Litinin ta wannan makon da muke cikiTsohon Shugaban ƙasar Nijeriya, Dokta. Goodluck Ebele Jonathan, ya ƙaddamar da ayyuka 18 waɗanda aka kammala su da Gwamnatin Jihar Bauchi ta yi na gina hanyoyin cikin garin na Bauchi.
Jonathan, wanda ya ƙaddamar da ayyukan a hanyar BRC 2-Yelwa, Bauchi, ya ce babu wasu al’ummar da za su ci gaban tattaliun arziki da shi ci gaban gaba ɗaya ba tare da abubuwan more rayuwa na zamani masu ɗorewa ingantattu, inda ya ce hanyoyi su me manyan abubuwan da suke samar da ci gaban kowace Jiha, saboda kuwa ai sun haɗa wurare ne masu yawa, bunƙasa harkokin kasuwanci, samar da damarmaki ga kuma bunƙasa kuwa ya san ana tafiya,tare da shi kan lamarin duk wani ci gaba.
Jonathan ya ce al’ummar Jihar ta Baucchi sun yi amanna da amincewa da Gwamna Bala Mohammed domin kuwa hakan ana iya ganewa akan yadda aka samu ci gaba a sassa daban daban na Jihar.
Ya ce,“Gwamna Bala Mohammed ba wai bane ya fara ire iren ayyukan na Shugabanci na gari ba saboda kuwa ayyukan da ya yi sun taɓa rayuwar al’umma.Ya ce yadda mulkin sa yake tafiyar da ayyukan da sukka shafi abubuwan more rayuwa, kamar harkar ilimi, kula da lafiyar al’umma,aikin gona,da kuma bunƙasa ak’umma ya nuna a fili ya nua a fili babban burin sa shi ne al’ummar Jihar Bauchi su ci gaba da samun ayyukan da za su nuna ana tafiya tare da kowa babu wanda aka manta da shi.”
Jonathan ya ƙara da cewa ba ya mamakin irin yadda Gwamnan ya yi ayyukan da suka samar da ci gaba, domin kuwa ya daɗe da sanin sa shekarun da suka gabata ya kuma san yadda yake da sha’awar yin ayyuka,mai da hankali sai ya cimma nasarar kammala ayyukan da yasa a gaban sa,domin samar da romon damukuraɗiyya ga al’umma domin samar da ci gaban su.
Yayi kira da al’ummar Bauchi su ci gaba da ba Gwamnatin haɗin kai domin a samu damar kare kare hanyoyin da aka ƙaddamar da kuma ayyukan jin daɗin al’umma da aka yi.
“Hanyoyi ba kawai wasu abu ba ne da ake gani da ido; tamkar hannun jari ne wanda aka yi saboda gaba.Sha’anin kulawa ana buƙatar haɗin kan duk ƴan Jihar ta Bauchi domin kulawa da su da kare su, wasu ayyuka ne, da ake san duk ƴan Jihar za su yi su don haka ne son bada haɗin kai kamar yadda ya jaddada,”.
Tsohon Shugaban ƙasa ya nuna jin daɗin sa da kuma tabbacin cewar Jihar za ta ci gaba ayyukan ci gaba masu ɗorewa ta hanyar kulawa da kuɗaɗen Jihar da kuma babban haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da al’ummar ta.
Tun farko da yake gabatar da na shi jawabin, Gwamna Bala Mohammed ya ce tun lokacin da ya fara mulkin sa, ya yanke shawarar zai fara da ayyukan da za su yi tasiri a rayuwar al’umman Jihar.
“Munsan cewa ingantattun hanyoyi suna da muhimmanci saboda sune suka haɗa al’ummomin wurare daban daban, suna bunƙasa harkar kasuwanci, bunƙasa yadda za a samu ilimi sa lamarin kula da lafiya, da kuma samar da dama wajen samun ci gaban da zai taimakawa ci gaban al’umma kamar yadda ya ƙata jaddadawa,”.














