Shugaban ƙungiyar masu sayar da ganye da kayan marmari na Kasuwar Utako Babban Birnin tarayya Hamza Mu’azu Karwai ya ce lokaci ya yi wanda za a fara ɗaukar mataki akan waɗanda suka ɗauki doka da kansu, ko kuma yanke hukunci wanda sau da yawa hakan yana kasancewa babbar matsala ko wata illa daga ƙarshe.
Hamza ya yi wannan maganar ne lokacin da yake faɗin albarkacin bakin sa dangane da irin waɗannan abubuwan da suke faruwa inda sau da yawa waɗanda su zauna gari banza ne suke ɗaukar irin matakin, na yin duk wani abinda duk suka ga dama wanda daga ƙarshe kuma abin yana cutar da duk wanda aka ɗauki irin matakin akan shi, ba tare da bincike ba. Ya ce ‘Abinda ke ɗaure ma shi kai, shi ne ba kasafai jami’an tsaro ke sa kansu cikin lamarin ba, bare ma su yi wani bincike’.
Ya ci gaba da bayani inda ya ce, ‘zai iya tunawa da maharba ƴan asalin Jihar Kano mutum 13 waɗanda suke kan hanyarsu ta komawa gida suna cikin mota daga Fatakwal, suna zuwa garin Uromi a Jihar Edo, a watan Maris 2025, suma haka aka tsaida motarsu duk da yake sun yi bayanin su maharba ne za su koma gida, amma haka ƴan ƙungiyar Bijilanti na gari suka kashe su tare da ƙonawa har yanzu, babu wani takamai man matakin da ya kamata a ɗauka kan su ba, haka abin ya tafi tamkar sabulu a cikin ruwa.’
Ya ce hakanan ma itam marigayiya Ummalkhairi Malama ce kuma Malamar makarantar Islamiyya a Marabar Jos, daga ta tambayi makarantar da ta yi niyyar zuwa hakanan sai wasu mata suke ce ita ce mai satar yara, ba tare da wani bincike ba, aka kashe ta tare da ƙona gawar ta.
Daga ƙarshe kuma ya yi kira da majalisun ƙasa dana Jihohi su yi doka ba tare da ɓta lokaci ba, duk kuma waɗanda suka ƙara aikata irin wannan laifi, dokar ta yi aiki akan su, abin kuma ya kasance babu sani babu sabo.














